Jami’an tsaro sun ƙarfafa tsaro a Jos

[ad_1]



An samu komawar yanayin zaman lafiya a Jos, babban birnin jihar Filato, biyo bayan sassaucin doka da aka samu a yankin ranar Laraba.

Wannan na zuwa ne yayin da aka tura jami’an tsaro daga hukumomi daban-daban zuwa unguwanni daban-daban a cikin babban birnin jihar domin daƙile sake faruwar abin da ya faru a ranar Larabar.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa, bayan sassauta dokar hana fita a ranar Laraba, wasu fusatattun matasa sun mamaye tituna, inda suka riƙa kai hari tare da kashe matafiya waɗanda ba su ji ba ba su gani ba, lamarin da ya janyo fargaba mai girma.

Wakilinmu wanda ya ziyarci babban birnin jihar a ranar Alhamis ya rawaito cewa, harkokin kasuwanci na komawa a hankali, inda aka ga ’yan kasuwa da masu sayayya suna gudanar da harkokinsu.

An ga motoci, babura masu ƙafa uku (keke NAPEP), babura da sauran hanyoyin sufuri suna zirga-zirga a kan hanyoyi.

An ga jibge jami’an tsaro masu yawa, inda sojoji, ’yan sanda, jami’an NSCDC, ’yan banga, da sauran jami’an tsaro aka tura su tare a babban tituna da wurare masu mahimmanci domin tabbatar da doka. An kuma ga sauran jami’an tsaro a cikin motoci suna sintiri daga shinge ɗaya zuwa wani, suna sintiri domin hana ɓarkewar rikicin.

Wasu ’yan kasuwa sun nuna jin daɗinsu kan wannan cigaba, suna masu fatan cewa abubuwa za su ci gaba da inganta.

Chukuemeka Christian, wani ɗan kasuwa a kusa da kasuwar Katako, ya yaba da matakan tsaron da aka ɗauka, yana mai cewa:

“Ina farin ciki da komai. Allah ne Ya sa abubuwan suka kasance haka. Idan ba don dokar hana fita ba, da lamarin ya yi muni sosai. Fargabar tana raguwa a hankali. Mun sha wahala lokacin dokar hana fita saboda babu abincin da za mu ci. Yanzu da muke kasuwa, za mu iya sayarwa mu kuma sayi abinci.”


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *