Sojoji Sun Ceto ‘Yan Mata 12 Da Boko Haram/ISWAP Suka Sace A Borno

[ad_1]


Rundunar Sojojin Nijeriya ta ce dakarunta na rundunar hadin gwiwa ta Operation Hadin Kai ta Arewa maso Gabas sun yi nasarar ceto ‘yan mata 12 da ‘yan ta’addan Boko Haram/ISWAP suka sace a gundumar Mussa da ke karamar hukumar Askira/Uba a jihar Borno.

Wata sanarwa da rundunar sojin Nijeriya ta fitar a shafukanta na sada zumunta, ta ce an sace ‘yan matan ne, wadanda shekarunsu ke tsakanin 15 zuwa 20, a ranar 23 ga Nuwamba yayin da suke girbin amfanin gona amma an ceto su a ranar Asabar, 29 ga Nuwamba, 2025.

A cewar sanarwar, an ceto ‘yan matan ne bayan wani samamen gaggawa da kwarewa da jami’an tsaro suka yi a yankin kudancin Borno.

An kwashe ‘yan matan da aka ceto zuwa wani sansanin soja mai tsaro inda suke samun kulawar lafiya.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *