Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Birnin Paris
[ad_1]
Da safiyar yau Lahadi, tawagogin Sin da Amurka sun gudanar da tattaunawa kan batutuwan da suka shafi tattalin arziki da cinikayya.
Mai magana da yawun ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Jumma’a cewa, bisa jagorancin muhimman yarjejeniyoyin da shugabannin kasashen biyu suka cimma a yayin ganawarsu a birnin Busan da kuma dukkan tattaunawa ta wayar tarho da aka yi a baya, bangarorin biyu za su yi shawarwari kan harkokin tattalin arziki da cinikayya da suke ci masu tuwo a kwarya.
Mataimakin firaministan kasar Sin He Lifeng, kuma mamban ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ne ya jagoranci tawagar kasar Sin. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
[ad_2]
Source link