Shugaban Xi Ya Karbi Sabbin Jakadun Kasashen Waje A Kasar Sin

[ad_1]

A yau Juma’a, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya karbi takardun sabbin jakadu 18 da aka turo kasar Sin.

Da yake jawabi ga jakadun, ya ce duniya a yanzu na fama da manyan sauye-sauye cikin sauri, irin wadanda ba kasafai ake gani ba, inda yanayin duniya ke kara fuskantar sauye-sauye da hargitsi da kalubale.

Ya kara da cewa rarrabuwar kawuna da fito-na-fito da cin nasara da faduwar wani bangare ba su da wata makoma, kuma dawo da amfani da karfi a duniya ba abu ne da jama’ar duniya ke son gani ba, yana mai cewa hadin kai da goyon bayan juna su ne kadai zabukan da suka dace. (FMM)

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *