Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

[ad_1]


Shugaban jam’iyyar APC na Kano, Abdullahi Abbas, ya nemi afuwar al’ummar Fagge bayan maganganunsa sun jawo fushi tare da haifar da ƙarar aikata laifuka da aka shigar a gaban kotun majistare a Kano. A cikin wani sauti da lauyan al’ummar Fagge, Barrister Abba Hikima Fagge, ya wallafa a Facebook, Abbas ya ce an yi kuskuren fahimtar abin da ya faɗa, yana mai jaddada cewa ba shi da wata hujja ta wulaƙanta mutanen Fagge.

Rahotanni sun nuna cewa mutane goma daga cikin fitattun mazauna Fagge sun shigar da ƙarar gaggawa suna zargin Abbas da yin kalaman tunzuri da ɓata suna. waɗanda suka shigar da ƙarar sun haɗa da Dr. Nuruddeen Abubakar, da Sheikh Abubakar Ya’u, da Alhaji Sani Salisu da wasu, bisa wakilcin kansu da sauran mutanen unguwar da ke son zaman lafiya. Sun buƙaci kotu ta ba da umarnin kamo Abdullahi Abbas ko kuma ta gayyace shi ya bayyana a gaban kotu.

Lauyoyin da suka shigar da ƙarar sun nemi kotu ta yi amfani da tanade-tanaden dokar ACJL 2019 domin umartar kwamishinan Ƴansanda na Kano ya binciki Abbas kan zarge-zargen da suka shafi cin mutunci, da haddasa kiyayya tsakanin wasu jama’a, da tunzura rikici da ɓata suna, waɗanda dukkansu suka saɓa wa kundin Penal Code na jihar.

An ce maganganun Abbas sun fito ne daga wani taron siyasa, inda aka ji yana danganta “duk wani mara ƙima” da Fagge, tare da wasu ƙarin kalamai da mazauna yankin suka ce suna iya haddasa rarrabuwar kai. Sai dai Abbas ya dage cewa an fassara kalamansa ba daidai ba, kuma bai yi nufin wulaƙanta wani ba.

Kotun majistare na shirin yanke hukunci kan bukatun da aka gabatar a cikin kwanaki kaɗan masu zuwa, idan kuma an amince da haƙirin da ya bayar, hakan na nufin za a iya janye ƙarar.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *