Shin Ko Lokacin Lashe Firimiyar Arsenal Ya Yi?

[ad_1]

A halin da ake ciki kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta bayar da tazarar maki 9 tsakaninta da Manchester City, yayinda take matsayi na daya a saman teburin gasar Firimiya ta kasar Ingila bayan buga wasan mako na 25.

Fiye da shekaru 20 kenan rabon da kungiyar dake birnin Landan ta lashe gasar Firimiya, a shekarar 2005 Arsenal ta samu nasarar lashe gasar ba tareda rashin nasara ko daya ba.

  • An Yi Taron Share Fage Na Shirin Talibijin Na CMG Na Murnar Sabuwar Shekara Bisa Kalandar Gargajiyar Sinawa A Addis Ababa
  • Kasuwar Musayar ‘Yan Kwallo: Yadda ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Canza Kungiyoyi

Duk da cewa kungiyar ta sha barar da damarmakin da ta samu na lashe gasar a shekaru biyu da suka gabata, amma a halin da ake ciki kungiyar wadda Mikel Arteta ke jagoranta ta cigaba da zage damtse wajen ganin ta faranta ran miliyoyin magoya bayan da take dasu a fadin Duniya.

Arsenal ta hada maki 56 da kwallaye 32 a wasanni 25 da ta buga, hakazalika ta samu nasara sau 17 ta buga canjaras 5 sannan aka doke ta sau 3 a wannan kakar da muke ciki.

Ba’a iya gasar Firimiya Arsenal ke kan teburi ba har ma da gasar zakarun Turai inda ta kare zagayen farko na rukuni a matsayi na daya, duba da cewa kungiyar ba ta taba lashe gasar zakarun Turai a tarihinta ba, wannan babbar dama ce gareta wajen ganin ta baiwa marada kunya.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *