NLC ta nemi ’yan Najeriya su yi watsi da dokokin haraji
[ad_1]
Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC), ta buƙaci ’yan Najeriya kada su amince da dokokin haraji da aka yi wa cushe.
Shugaban NLC, Joe Ajaero ne, ya bayyana a saƙonsa na Kirsimeti na 2025, inda ya ce an yi wa wasu dokokin harajin cush ko sauye-sauye.
Ya ce, “Dole ne mu nemi adalci a kan haraji, inda masu kuɗi su biya nasu, kuma a cire duk wani haraji da ke ci wa talakawa.
“Duk wata doka ta haraji da aka sauya ko aka yi wa cushe, kada a amince da ita.”
Ajaero, ya ƙara da cewa, yana da kyau a tsara doka cikin tsari maimakon a gaggauta yin ta ɗauke da kurakurai.
Har ila yau, ya bukaci ’yan Najeriya su kasance masu haɗin kai wajen neman adalci a al’amuran da suka shafi mulki.
Tuni dai Majalisar Wakilai ta fara bincike kan wasu dokokin harajin da aka yi wa sauye-sauye.
Kwamitin da Muktar Aliyu Betara ke jagoranta, ya fara bincike a ranar 23 ga watan Disamba.
Kwamitin ya ce zai ƙoƙarin kammala binciken a kan lokaci, tare da gabatar da rahotonsa.
Masu alaƙa
[ad_2]
Source link