Nijar Ta Haramta Fitar Da Dabbobi Ketare Don Takaita Karancinsu A Cikin Gida
[ad_1]
Gwamnatin jamhuriyar Nijar ta sanar da hana fitar da dabbobi zuwa kasashen ketare a wani yunkuri na samar da wadatuwar dabbobin a cikin gida, wannan mataki dai shi ne irinsa na biyu da aka dauka a ‘yan shekarun nan cikin wannan kasa dimbin jama’arta ke harkokin kiwon dabbobi don sayarwa.
Sai dai tuni wannan mataki ya gamu da suka daga ‘yan kasuwa da masu turkar dabbobin domin sayarwa bayan da suka bayyana cewa kai tsaye matakin zai iya haifar musu da asara mai yawa musamman a lokacin sallar layya.
- Tinubu Ya Kaddamar Da Shirin Aikin Noma Domin Samar Da Wadataccen Abinci
- Ministan Wajen Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Kawo Karshen Matakan Soji A Gabas Ta Tsakiya
Nepal: Mawakin Gambara Na Dab Da Lashe Zaben Shugabancin Kasar
Tsohon mawakin gambara Balendra Shah yana gab da samun gagarumar nasara a babban zaben Nepal, inda jam’iyyarsa ta Rastriya Swatantra ke kan gaba.
Sakamakon farko na nuna yadda matasa suka yi watsi da tsofaffin ‘yan siyasa, wanda hakan ke zama babban sauyi a tsarin mulkin kasar. A halin yanzu, Shah na ba wa tsohon Firayim Minista KP Sharma Oli rata mai nisa, lamarin da masu nazari ke kallo a matsayin sakamakon zanga-zangar yaki da cin hanci da rashawa da ta gudana a kasar.
Ana ganin wannan nasara a matsayin bukatar jama’a ta samun sabon jini da sauyi na gaske a siyasar Nepal. Yayin da ake ci gaba da kirga kuri’u, magoya baya na murna a Kathmandu, ana kuma sa ran bayyana sakamakon karshe nan da 9 ga watan Maris.
Nasarar ka iya bai wa jam’iyyar RSP damar kafa gwamnati mai karfi don aiwatar da sauye-sauyen da aka yi alkawari.
[ad_2]
Source link