Mutum 23 Sun Mutu, 146 Sun Jikkata A Fashewar Bama-bamai A Maiduguri

[ad_1]

Aƙalla mutane 23 sun mutu yayin da wasu 146 suka samu raunuka sakamakon jerin fashewar bama-bamai da suka girgiza birnin Maiduguri, babban birnin jihar Borno, a daren Litinin.

Fashe-fashen sun faru ne a ƙofar shiga ta Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH), Kasuwar Litinin da kuma yankin Ofishin Wasiku na tsohon birnin.

  • Ko Za A Ga Sauyi Bayan Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka?
  • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 26

Surajo Abdullahi, mai kula da shiyyar Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA), wanda ya tabbatar da alkaluman, ya ce an kwashe mutane 169 zuwa asibitoci uku a Maiduguri.

“Mutane 108 na karɓar magani a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH), 20 a Asibitin Umaru Shehu, sannan 17 a Asibitin Kwararru na Maiduguri,” in ji shi.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *