Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Sace Adaidaita Sahu A Borno

[ad_1]

Rundunar ’Yansandan Jihar Borno, ta kama wasu mutane biyu bisa zargin satar adaidaita sahu a unguwar Jajeri da ke Maiduguri.

Kakakin rundunar, ASP Nahum Daso, ya ce lamarin ya faru ne a ranar 4 ga watan Agusta, 2025, lokacin da wani Abubakar Tijani ya kai rahoton cewa an sace mass adaidaita sahu.

Bayan rahoton, rundunar Crack Squad ta kama wasu mutum biyu; Yakubu Musa da Adamu Musa, dukkaninsu daga Jajeri.

Lokacin gudanar da bincike, sun amsa laifin, kuma an samo adaidaita sahun a wajensu.

Kwamishinan ’Yansandan jihar, Naziru Abdulmajid, ya yaba wa jami’an bisa jajircewarsu tare da tabbatar wa jama’a cewa ’yansanda za su ci gaba da yaƙi da laifuka a jihar.

Ya kuma roƙi jama’a da su ci gaba da ba da sahihan bayanai don taimakawa wajen tabbatar da tsaro a jihar.




Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp



[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *