Mauludi: Ƙungiyoyin addini sun nemi gwamnati ta sassauta dokar hana hawa babur a Gombe

[ad_1]



Ƙungiyoyin makarantu da na addinin Musulunci a Jihar Gombe, sun roƙi gwamnatin jihar da ta sassauta dokar taƙaita hawa babur daga ƙarfe 7 na yamma zuwa 6 na safe, domin sauƙaƙa zirga-zirga yayin bukukuwan Mauludi.

Shugaban ƙungiyar makarantun Islamiyya na Jihar, Alhaji Muhammadu Nuhu, ya ce yawancin masu zuwa wajen bukukuwan na amfani da babura ne.

Ya ce ana kammala bukukuwan da misalin ƙarfe 10 na dare, amma dokar tana fara aiki tun 7 na yamma, don haka suka roƙi a sassauta dokar saboda muhimmancin Mauludi.

Alhaji Nuhu, ya gode wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa tallafin da ya bayar wajen shirya taron, da kuma tabbatar da tsaro.

Shi ma shugaban Fityanul Islam a jihar, Sheikh Bashir Ladan, ya ce bikin Mauludi na nuni da ƙaunar Manzon Allah (SAW), kuma yana ƙunshe da addu’o’in zaman lafiya da haɗin kai a ƙasar nan.

Haka kuma, shugaban Majma’ul Madarasatul Islamiya, Malam Muhammad Aminu Salisu, ya ƙara da rokon gwamnati ta sassauta dokar domin kada a hana mutane halartar Mauludin bana.

Ya ce sun tattauna da jami’an tsaro kuma an tanadi matakan tabbatar da zaman lafiya a yayin taron.

Ƙungiyoyin sun jaddada cewa dokar hana hawa babura ta sa wasu jin tsoro, wanda hakan ya rage yawan mahalarta jerin gwanon Mauludi.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *