Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha
[ad_1]
Ofishin magatakardar majalisar tarayya ya fayyace iya matsayinsa kan rikicin da ya dabaibaye dakatarwar da aka yi wa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, inda ya ce, ‘yan majalisar ne kadai ke da hurumin dawo da ‘yar majalisar da aka dakatar.
Babban magatakardar, a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin a Abuja ta hannun Daraktan Yada Labarai, Mista Bullah Audu Bi-Allah, ya jaddada cewa ofishin yana gudanar da ayyukansa ne a matsayin hukumar gudanarwa ba tare da ikon sauyawa ko gyara hukuncin da Majalisar Dattawa ta yanke ba.
A cewar sanarwar, “Ofishin magatakarda ba shi da ikon yin bita, hanawa ko sauya hukuncin Majalisar Dattawa.”
Majalisar dattawa ta dakatar da Sanata Akpoti-Uduaghan a ranar 6 ga Maris, 2025, na tsawon watanni shida. Duk da cewa an kalubalanci lamarin a kotu, amma babbar kotun tarayya ba ta bayar da wani umarni na soke dakatarwar ba ko kuma tilasta sake dawo da ita bakin aiki.
A ranar 4 ga Satumba, 2025, Sanatar ta sanar da ofishin magatakarda akan aniyar ta na ci gaba da ayyukan majalisa, nan take, ofishin ya mika wasikar ga shugabannin majalisar dattawan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp
[ad_2]
Source link