Kwalara ta kashe fursunoni 11 a Congo

[ad_1]



Aƙalla fursunoni 11 ne suka mutu, yayin da wasu da dama ke fama da jinya bayan kamuwa da cutar kwalara a wani gidan yari da ke yammacin ƙasar Jamhuriyyar Dimokuraɗiyar Congo, kamar yadda ma’aikatar shari’a ta ƙasar ta bayyana a ranar Litinin.

Ministan Shari’a, Guillaume Ngefa, ya ce an tabbatar da barkewar cutar ne a ranar 27 ga Maris a gidan yarin da ke garin Mbanza-Ngungu na lardin Kongo Central, kimanin kilomita 150 daga birnin Kinshasa.

A cewarsa, zuwa yanzu mutane 11 sun mutu sakamakon cutar, yayin da aka samu aƙalla mutane 74 da suka kamu daga cikin fursunoni kusan 800 da ke gidan yarin.

Hukumomi sun tura tawagar likitoci domin kula da marasa lafiya tare da ɗaukar matakan kariya, ciki har da allurar rigakafi da kuma tsaftace muhalli.

Haka kuma, gwamnati ta sanar da ɗaukar matakan tsaftace muhalli da kashe ƙwayoyin cuta, sa ido kan ingancin ruwan sha, da kuma dakatar da karɓar sabbin fursunoni na ɗan lokaci.

Rahotanni sun nuna cewa yawancin gidajen yarin sun tsufa waɗanda aka gina tun a zamanin mulkin mallakar da Belgium ta yi wa ƙasar.

Haka kuma gidajen yarin suna fama da cunkoso, ƙarancin ruwa mai tsafta da rashin ingantattun wuraren kwana, abubuwan da ke taimakawa wajen saurin yaɗuwar cututtuka kamar kwalara.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *