Kashi 60% Na Ƴan Nijeriya Ne Ke Samun Ƙasa Da ₦100,000 – Rahoto
[ad_1]
Wani rahoto na Piggyvest na shekarar 2025 ya nuna cewa kusan kashi 60% na ƴan Nijeriya na samun ƙasa da N100,000 wasu ma basu da kuɗin shiga. Rahoton ya kuma nuna matsin tattalin arziƙi na ƙara tsananta ga gidaje.
Rahoton ya bayyana cewa hauhawar farashi na rage ƙarfin saye duk da ƙarin albashi a zahiri. Ya jaddada cewa mutane na samun ƙarin kuɗi amma ba sa iya biyan buƙatunsu kamar da.
- Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Tallafa Wa Talakawa Tare Da Inganta Haɗin Kai
- NiMet Ta Yi Hasashen Ƙwallewar Rana Da Gajimare Na Kwana Uku, Litinin – Talata
Odun Eweniyi ta ce raguwar darajar Naira ce ke haddasa wannan matsalar. Ta bayyana cewa hauhawar farashi ya haura kashi 33% a 2024, wanda ya rage tasirin kuɗin shiga.
Rahoton ya kuma nuna cewa matasa da mata sun fi kasancewa a ƙananan rukunin masu ƙaramin albashi. Haka kuma yawancin gidaje na dogaro da tushen kuɗi guda ɗaya ne kawai.
An kuma nuna cewa yawancin kuɗin shiga na tafiya ne wajen abinci, da sufuri da masauki (haya). Haka kuma mutane da dama na tallafa wa ƴan uwa, abin da ake ƙara nauyi akan kuɗin shigar da suke samu.
Rahoton ya ƙara da cewa rabin ƴan Nijeriya ba sa iya ajiyar kuɗi kwata-kwata. Ya jaddada cewa rashin tabbas a tattalin arziƙi na sa mutane fifita kashe kuɗi kan buƙatu na gaggawa.
Duk da haka, rahoton ya ce ƴan Nijeriya na ci gaba da nuna juriya ta hanyar ƙarin sana’o’i da tsara kashe kuɗi. Sai dai ya yi gargaɗi cewa rashin kuɗi na ci gaba da ƙaruwa a ƙasar.
[ad_2]
Source link