Karfin Sin A Fannin Kere-kere Na Taimakawa Nahiyar Afrika Komawa Ga Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

[ad_1]

Ministan kula da harkokin makamashi na kasar Madagascar, Ny Ando Ralitera, ya ce karfin kere-kere da kasar Sin take da shi a bangaren makamashi mai tsafta, ya taimaka wajen gaggauta komawar kasashen nahiyar Afrika ga amfani da makamshi mai tsafta.

Da yake hira da kamfanin dillancin labarai na Xinhua a ranar Alhamis, a gefen taron kungiyar raya yankin kudancin Afrika (SADC) na Makon Makamashi mai Dorewa, a birnin Victoria Falls na Zimbabwe, Ralitera ya ce kayayyakin kasar Sin masu arha da matukar gogewar da kasar ke da ita a bangaren makamashi mai tsafta, sun samar wa nahiyar Afrika gagagrumin taimako.

A cewarsa, Madagascar na hada hannu sosai da Sin a bangaren samar da lantarki da makamashi. (FMM)

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *