Jami’an tsaro na iya kama ɗan uwan mai laifi idan ba a samu mai laifin ba — Lauya

[ad_1]



Wata fitacciyar lauya a Kano, Barista Asiya Muhammad Imam, wacce ke aiki a ofishin lauyoyin gwamnatin Jihar Kano da ke Gidan Murtala, ta ce doka ba ta bai wa jami’an tsaro kama ɗan uwan mai laifi idan ba a samu mai laifin ba.

Barista Asiya ta bayyana haka a yayin wani taron wayar da kan al’umma da Cibiyar Isa Wali da ke kare muradun mata, yara, matasa da nakasassu a birnin Kano da kewaye ta shirya a ranar Alhamis a unguwar Rimin Keɓe da ke ƙaramar hukumar Ungogo a jihar.

Taron wanda ya ƙunshi nakasassu daban-daban da mata ya mayar da hankali kan tanade-tanaden Dokar ACJL ta Jihar Kano ta 2019 a ƙarƙashin shirin samar da adalci ga kowa na Justice for All (II).

A yayin taron an yi kira ga iyaye mata da su daina ɓoye laifin ’ya’yansu idan tsautsayi ya auku domin inganta tarbiyyar al’umma.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *