Gwamnonin Arewa Sun Yi Allah-Wadai Da Harin Kasuwar Neja
[ad_1]
Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) ta yi kakkausar suka kan harin ta’addanci da ya yi sanadin mutuwar akalla ƴan kasuwa 30 a Kasuwar Daji da ke Karamar Hukumar Borgu a Jihar Nijar. Kungiyar ta bayyana harin a matsayin mummunar ta’asa da aka aikata kan fararen hula masu neman halal, tare da zama babbar barazana ga zaman lafiya da hanyoyin dogaro da kai a yankin.
Rahotanni sun nuna cewa harin ya yi sanadin kisan mata da sauran ƴan kasuwa da dama, yayin da aka sace wasu da kuma kona kasuwar baki daya, lamarin da ya jefa al’ummomin yankin cikin jimami da fargaba. Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana matukar kaɗuwa kan lamarin, yana mai cewa ya jawo baƙin ciki mai tarin yawa, ya tsaida harkokin tattalin arziƙi, tare da tayar da hankalin al’ummomin da ke zaune lafiya.
- Tinubu Ya Sha Alwashin Adalci Ga Waɗanda Aka Kashe A Kasuwar Neja
- Yadda Aka Sako Ɗaliban Makaranta 130 Da Aka Sace A Jihar Neja
A cikin sanarwar da Darakta Janar na Yaɗa Labarai, Isma’ila Uba Misilli, ya sanya wa hannu, Gwamna Yahaya ya jaddada cewa irin wadannan ayyukan ta’addanci da ake kai wa mata ƴan kasuwa da sauran ƴan ƙasa masu neman halal abin ƙyama ne gaya, kuma suna raunana dankwafar da al’umma da tattalin arziƙin yankin Arewa. Ya kuma buƙaci hukumomin tsaro da su ƙara ƙaimi wajen gano tare da cafke waɗanda suka aikata harin domin gurfanar da su a gaban shari’a.
Kungiyar ta miƙa saƙon ta’aziyyarta ga iyalan waɗanda suka rasu, da Gwamnati da al’ummar Jihar Neja, tare da yin addu’ar samun rahamar Allah ga waɗanda suka mutu da kuma fatan gaggauta ceto waɗanda aka sace.
Haka kuma, Ƙungiyar Gwamnonin Arewa ta jajanta kan hatsarin kwale-kwale da ya faru a garin Garbi da ke Ƙaramar Hukumar Nguru a Jihar Yobe, inda aƙalla mutane 25 suka mutu yayin da wasu 14 suka ɓace, tana mai kira ga hukumomi da su ƙara ƙaimi wajen aikin ceto da kuma tsaurara matakan tsaro a harkokin sufuri domin kauce wa maimaita irin wannan masifa.
[ad_2]
Source link