Gwamnatin Sakkwato ta bayar da umarnin biyan ma’aikata albashi
[ad_1]
Gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu ya bayar da umarnin biyan ma’aikatan jihar albashin watan Fabarairu nan take, saboda ƙaratowar watan azumin watan Ramadan.
Gwamnan wanda ya sanar da hakan ne a cikin wata sanarwa ta hannun shugaban sashen yaxa labarai da hulɗa da jama’a na ofishin gwamnan, Abubakar Bawa a yau Alhamis.
Sanarwar ta qara da cewa, matakin ya shafi: “ma’aikatan Gwamnatin jiha, ƙananan hukumomi da ma’aikatan hukumar Ilimi ta ƙananan hukumomi, da kuma tsofaffin ma’aikata masu karɓar fansho a duk faɗin jihar”.
Bayanin ya ƙara da cewa, matakin fara biyan albashin zai fara aiki ne daga ranar Juma’a 13 ga watan na Fabarairu.
Masu alaƙa
[ad_2]
Source link