Gwamnatin Filato Ta Sanya Dokar Hana Fita Ta Sa’o’i 48 A Jos Ta Arewa

[ad_1]

Gwamnatin Jihar Filato ta sanar da ƙaddamar da dokar hana fita ta sa’o’i 48 a Jos ta Arewa. Matakin ya biyo bayan wani hari da ya auku a Gari Ya Waje ranar Lahadi, 29 ga Maris, 2026.

A cewar sanarwar, dokar za ta fara aiki daga ƙarfe 12 na dare na 29 ga Maris. Za ta ƙare ranar 1 ga Afrilu, 2026, domin bai wa jami’an tsaro damar daidaita al’amura.

  • Xi Ya Taya Jose Antonio Kast Murnar Lashe Zaben Shugaban Chile
  • An Sallami Anthony Joshua Daga Asibiti Bayan Hatsarin Mota

Gwamnatin jihar, ƙarƙashin jagorancin Gwamna Caleb Mutfwang, ta yi Allah-wadai da harin. Ta ce za a kamo masu hannu  cikinsa tare da gurfanar da su gaban shari’a.

Hukumomi sun buƙaci jama’a su kwantar da hankula su kuma bi umarnin tsaro. An roƙe su su ba da bayanai masu amfani don taimaka wa bincike.

Sanarwar da Kwamishinar Yaɗa Labarai, Joyce Ramnap, ta sanya wa hannu ta jaddada ƙudirin gwamnati na kare rayuka da dukiyoyi.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *