Gwamnatin Bauchi Ta Nemi Agajin Tinubu Game Da Yaƙi Da Ta’addanci

[ad_1]

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya buƙaci gwamnatin tarayya, ta gaggauta shiga tsakani tare da ƙarfafa tallafin tsaro, biyo bayan wani ƙazamin hari da Ƴan bindiga suka kai a yankin Kafin Duguri, inda aka kashe mazauna garin tare da jikkata wasu.

Gwamnan, ya yi wannan roƙo ne a lokacin da ya kai ziyarar jajantawa al’umma, inda ya bayyana harin a matsayin wani babban ƙalubalen tsaro da ya mamaye cibiyoyin tsaro na yankin.

Ya ƙara da cewa, hukumomin tsaro a ƙasa suna buƙatar ƙarin nagartattun makamai da tallafin kayan aiki, domin tunkarar Ƴanbindigar da suka mamaye sassan yankin.

  • Me Ya Haifar Da Abubuwan Bakin Cikin Da Ke Faruwa A Minneapolis
  • Rasmus Højlund Ya Sauya Sheƙa Zuwa Napoli A Matsayin Aro Daga Manchester United

Gwamna Mohammed ya bayyana cewa, yayin da yake wata ziyarar aiki a Abuja, ya yi wa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bayanin halin da ake ciki. A cewarsa, shugaban ƙasar a matsayinsa na babban kwamandan sojojin ƙasar, ya jajantawa iyalan waɗanda lamarin ya shafa tare da tabbatar wa al’ummar ƙasar goyon bayan gwamnatin tarayya, domin dawo da zaman lafiya.

Da yake yaba wa wannan bajinta ta mazauna Kafin Duguri, gwamnan ya ce; mutanen sun nuna jajircewar da ba a saba gani ba, musamman wajen tunkarar harin, lamarin da ya tilasta wa maharan ja da baya.

Har ila yau, ya kuma yi nuni da cewa; duk da cewa, an yi asarar rayuka da jikkata wasu daga cikin mazauna yankin, amma tsayin-dakan da al’ummar yankin suka yi, ya nuna matuƙar haɗin kai da tsayin daka da kuma kishin ƙasa ga kakanninsu.

Mohammed ya bayyana cewa, an daƙile ayyukan Ƴan bindiga a wasu sassan jihar da suka haɗa da Ƙananan Hukumomin Ningi da Jama’are da kuma Bogoro, amma ya bayyana ci gaba da kai hare-hare a yankinsa na Duguri a matsayin abu maras daɗi.

Ya kuma bai wa mazauna jihar tabbacin cewa, gwamnati ta ɗauki aniyar kawar da masu aikata laifuka gaba-ɗaya a faɗin jihar.

Da yake yin ƙarin haske kan muhimmancin tattalin arziƙin yankin, gwamnan ya ce; Kafin Duguri, yana da arziƙin ƙasa mai albarka da amfanin gona da kuma albarkatun ƙasa, yana mai jaddada cewa; mazauna yankin sun dogara ne da noma sosai, domin rayuwarsu.

Ya ƙara da cewa, ayyukan samar da ababen more rayuwa da ake ci gaba da yi da suka haɗa da gina tituna da ke haɗa al’umma da yankunan da ke maƙwabtaka da su, za su ci gaba da ci gaba duk da ƙalubalen tsaron da ake da shi.

A wani mataki na ɗaukar matakan gaggawa, Gwamna Mohammed ya bayyana shirin ɗaukar sabbin Ƴan banga da kuma horar da su tare da haɗin gwiwar Ƴansanda.

Ya kuma bayar da tabbacin cewa, Gwamnatin Jihar Bauchi, ta ɗauki cikakken alhakin kula da waɗanda suka jikkata, yayin da aka gudanar da addu’o’in samun rahama ga waɗanda suka rasa rayukansu a harin.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *