Gwamnati ta ƙaryata CAN da al’ummar Kajuru
[ad_1]
Taƙaddama ta ɓarke bayan al’umma da Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) sun bayar da rahoton garkuwa da mutane 160 a wani coci da ke ƙauyen Karnin Wali a Ƙaramar Hukumar Gajuru da ke Jihar Kaduna.
A ɗaya ɓangaren kuma, Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Kaduna ta ƙaryata rahoton, da cewa babu wani abu kamar haka da ya faru a jihar.
A cewar CAN da shugabannin al’umma, lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:00 na safe a Cocin ECWA da Seraphim–Cherubim. An ce wasu mutane goma sha ɗaya sun samu nasarar tserewa daga hannun masu garkuwa da su.
Al’ummar yankin sun daɗe suna fuskantar hare-hare daga ’yan bindiga da ke addabar su tun daga shekarar 2018
Dakacin ƙuye ya tsere daga hannun mahara
Dakacin Kurmin Wali, Ishaku Ɗan’azumi, ya bayyana yadda ya tsira da kyar bayan ’yan bindiga sun yi garkuwa da shi. Ya shaida wa wakilinmu ta waya cewa, maharan da suka zo a kafa dauke da bindigogi sun sace mutane 177, amma mutum goma sha ɗaya sun tsere.
“Yanzu mutane 166 suna hannunsu maza, mata da yara. Wannan ba shi ne karo na farko da suka kai mana hari. Daga lissafina, sun kai hari garinmu kusan sau 23 tun daga 2018,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa, a hare-haren baya yawanci ana satar mutum ɗaya zuwa biyar ne, amma wannan shi ne karo na farko da aka sace fiye da mutum ɗari lokaci guda.
Ɗan’azumi ya kuma ce mako guda kafin wannan hari, ’yan bindigar sun sace mutane 21, daga bisani aka sake su bayan an biya kuɗin fansa, sai kuma suka dawo ranar Lahadi suka sake sace wasu.
Yana bayyana wahalar da suka sha, da cewa: “Sun dinga dukan mu da sanduna. Da zarar mutum ya faɗa hannunsu, abin da ya rage masa addu’a ne.”
Ya bayyana cewa yawancin mazauna suna kwana a daji da dare, sannan ya roƙi gwamnati da ta kawo agajin gaggawa, yana mai cewa al’ummar “ta nutse cikin bashi” sakamakon hare-hare da ake kai musu akai-akai.
Ya yaba wa jami’an tsaro bisa ziyarar da suka kai wa al’ummar bayan harin, yana cewa Shugaban Ƙaramar Hukuma, sojoji da ’yan sanda sun ziyarci ƙauyen domin duba halin da ake ciki.
Ƙungiyar CAN ta tabbatar da harin
Shugaban CAN na Jihohin Arewa 19, Rabaran Joseph John Hayab, ya tabbatar da faruwar lamarin ga wakilinmu tare da bayyana shi a matsayin abin baƙin ciki.
Ya ce cocin guda biyu ne harin ya shafa, kuma ko da yake bai so ya ambaci adadin mutanen da aka sace ba, halin da ake ciki abin damuwa ne.
Ya ce, “Ba na son magana kan alƙaluman, amma bayanin da na samu daga yankin shi ne an ce mutane 172, mutum 9 sun tsere, sauran 163 suna hannun masu garkuwa da su.”
Ya ƙara da cewa, “Abu ne mai tsanani da baƙin ciki, amma ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba. Hukumomin tsaro da gwamnati suna ƙoƙarinsu wajen dawo da zaman lafiya a Kaduna, kuma muna farin ciki da hakan.”
Ya ce, “Amma na san wannan sabon shingen mugunta duk abin da dalilinsa ba zai sa mu haƙura ba. Muna son yin aiki tare da hukumomin tsaro da gwamnati domin tabbatar da cewa an dawo da waɗannan mutane.”
Ya ci gaba da cewa, “Wannan shi ne abin da muke so duniya ta sani: za mu yi aiki da hukumomin tsaro da gwamnati domin tabbatar da dawowar waɗannan mutane.
“Mun san irin ƙoƙarin da hukumomin tsaro da gwamnati ke yi domin dawo da zaman lafiya, don haka ba za mu riƙa zargin mutane ba kan abin da muka san suna ƙoƙarinsu.”
Ya kuma ce, “Idan su (’yan bindiga) suna yin haka ne domin tayar da fushi, za su yi mamaki. Za mu dawo da mutanenmu, kamar yadda ake dawo da wasu a kwanakin nan. Waɗannan mutane ma za su dawo.”
’Yan sanda sun ƙaryata sace mutanen
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kaduna, CP Rabiu Muhammad, ya ƙaryata rahotannin sace mutane da yawa a Kurmin Wali.
A cewarsa, “An gaggauta haɗa jami’an tsaro bayan samun bayanin wani zargin hari daga ’yan bindiga.
“’Yan sanda, sojoji da sauran jami’an tsaro tare da Shugaban Ƙaramar Hukuma sun ziyarci al’ummar, amma ba su samu wata hujja da ke tabbatar da ikirarin ba.
“Har zuwa yanzu, babu wanda ya iya bayar da sunan ko mutum ɗaya da aka ce an sace daga wannan al’umma,” in ji CP Rabiu.
Ya ƙara da cewa babu wani bayani kan hari ko sace fiye da mutane 300 kamar yadda aka ruwaito. Ya kuma gargaɗi masu yaɗa labaran ƙarya da su daina, yana mai jaddada cewa jami’an tsaro a shirye suke a kodayaushe domin magance barazanar gaske.
“Idan ba su daina irin wannan ta’adi ba, za mu kama duk wanda aka samu da laifi mu hukunta shi bisa doka,” in ji shi.
CP Rabi’u ya buƙaci duk wanda ke da iƙirarin akasin haka da ya fito da sunaye da hujjoji na gaskiya na mutanen da ake zargin an sace.
Ba a kai hari ba, in ji Ciyaman
Shugaban Ƙaramar Hukumar Kajuru, Dauda Madaki, shi ma ya ƙaryata rahotannin harin a Kurmin Wali, yana mai kiran su jita-jita.
Da yake magana a ranar Litinin bayan tarurrukan tsaro a Gidan Gwamnati, Madaki ya ce da kansa ya ziyarci yankin bayan jin rahotannin, tare da jami’an tsaro da suka haɗa da ’yan Sanda da sojoji da DSS da sauran jami’an tsaro na musamman.
Ya ce bayan isarsu, al’ummar na cikin kwanciyar hankali kuma komai yana tafiya yadda ya kamata.
Shugaban ya tabbatar da cewa an ziyarci cocin da aka ambata a cikin jita-jitar, amma ba a samu wata hujjar hari ba. Tattaunawa da shugabannin ƙauyuka ma ta tabbatar da cewa komai lafiya, in ji shi.
Shugabannin ƙauyen sun bayyana cewa damuwarsu ta samo asali ne daga wani lamari da ya faru kwanaki uku baya, inda sojoji suka kori wasu mutane a kusa da Dutsen Agula.
Madaki ya ce ya nemi sunayen duk wanda ake zargin abin ya shafa, amma babu wanda aka bayar da sunansa.
“Iyakar saninmu, babu wanda ke asibiti sakamakon wannan abin da ake kira hari. Saboda haka, na yi imanin wannan jita-jita ce da wasu ke yaɗawa,” in ji shi.
Ya bukaci mazauna da jama’a da su bayar da sahihin bayani idan har an sace wani, yana mai jaddada cewa duk da tambayoyi da aka yi, babu sunayen da aka gabatar.
Ya ƙara da cewa tabbatar da zaman lafiya a Kajuru na daga cikin muhimman abubuwan da ake bai wa fifiko, kuma ko da yake ba a kai matsayin da ake so ba, yanayin tsaro ya inganta fiye da da.
Madaki ya kammala da cewa, “Iyakar sanina, ina nan ne domin tabbatar da cewa babu wani hari da ya faru.”
Gwamnatin Nijar Kaduna ta ƙaryata harin
A martaninsa, Kwamishinan Tsaron Ciki da Harkokin Gida, Sule Shaibu (SAN), ya ce Shugaban CAN da sauran shugabannin addini sun yi gana da mutanen yankin da ake zargin an yi sace-sacen.
“Sun gano cewa abin da aka fitar zuwa fili ga jama’a gaba ɗaya ba gaskiya ba ne,” in ji shi, yana mai tabbatar da cewa “Gwamnatin Jihar Kaduna ba ta da sassauci ko kaɗan ga aikata laifuka.”
Masu alaƙa
[ad_2]
Source link