Gwamnati Na Tuhumar Malami Da Ɗansa Kan Laifuka 16 Na Almundahanar Kuɗaɗe

[ad_1]

Gwamnatin Tarayya ta shigar da ƙarar tuhuma 16 kan tsohon Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, SAN, kan zargin karkatar da kuɗaɗen almundahana da suka kai biliyoyin naira.

A takardar ƙarar, wacce aka shigar a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta haɗa da ɗan Malami, Abubakar Abdulaziz Malami, da Bashir Asabe, ma’aikaciyar Rahamaniyya Properties Limited, a matsayin waɗanda ake tuhuma tare.

A cewar takardar tuhumar mai lamba FHC/ABJ/CR/700/2025, Gwamnatin Tarayya ta zargi tsohon ministan da waɗanda ake tuhuma tare da shi da amfani da kamfanoni don ɓoye asalin yadda kuɗaɗen haram ɗin suka samo asali, tsakanin Yuli 2022 da Yuni 2025.

Gwamnati ta ce, laifukan sun saɓa wa tanadi da yawa na dokar kuɗi, ta 2011 da 2022, kuma za a iya hukunta su a ƙarƙashin tanadin dokar.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *