El-Rufai Ya Koma Kotu Bayan Rasuwar Mahaifiyarsa
[ad_1]
Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya koma Kotun Tarayya da ke Kaduna, inda ake sa ran za a saurari buƙatar ba da belinsa.
Hukumar ICPC ta gurfanar da shi a kotu kan tuhume-tuhume guda 10, ciki har da zargin karkatar da kadarorin gwamnati da kuma almundahanar kuɗaɗe.
- Sauya Sheƙar Gawuna Zuwa ADC Babban Koma Baya Ne Ga APC – Bashir Ahmad
- Gawuna, Ya Yi Murabus Daga Shugabancin Hukumar FMBN Gabanin Shiga ADC
El-Rufai ya bayyana a gaban kotu bayan shafe sama da wata guda a tsare.
Tun da farko, kotun ta sanya ranar 31 ga watan Maris, 2026 domin sauraron buƙatar bayar da belinsa.
An sake shi a ranar 27 ga watan Maris bisa dalilai tausayawa, bayan rasuwar mahaifiyarsa a birnin Cairo na ƙasar Masar.
[ad_2]
Source link