Dilar kwaya ta mutu ana shari’arta a kotu
[ad_1]
Wata mata da ake zargi da dillancin miyagun kwayoyi ta mutu jim kadan bayan an gurfanar da ita a gaban kotu.
Dubun matar mai shekaru 52 ta cika ne bayan da fada hannun jami’an kwamitin aiki da cikawa na Jihar Edo a yayin da take sayar da kayan da ake zargin miyagun kwayoyi ne.
Daga bisani jami’an suka mika ta ga Hukumar Yaki da Miyagun Kwayoyi (NDLEA) domin gurfanarwa a gaban kotu.
Shaidu a kotun sun ce an ga alamar rashin koshin lafiya a tattare da matar a lokacin da jami’an hukumar suka kai ta kotu, lamarin da suka bayyana a matsayin rashin kulawa.
Wata majiya ta ce tun watan Janairu Hukumar NDLEA take tsare da matar take matar ba tare da an gurfanar da ita a kotu ba.
Dan marigayiyar, mai suna Samuel, ya bayyana cewa sun sha rokon hukumar ta gurfanar da ita a kotu. Ya ce, a ranar Litinin ya kamata a gurfanar da ita, amma ranar Talata ta yanke jiki a cikin kotu ta ce ga garinku nan.
Sai dai Kwamandan Hukumar NDLEA a Jihar Edo, Mitchell Ofoyeju, ya musanta zargin mutuwar wadda ake zargin yana da nasaba da sakaci daga bangaren jami’ansa.
Masu alaƙa
[ad_2]
Source link