Category: Latest News

  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Katsina

    [ad_1]

    Dakarun Sojin Nijeriya sun kashe ‘yan bindiga 45 da suka kai hari ƙauyen Alhazawa a Jihar Katsina.

    Jami’an gwamnati a jihar sun ce lamarin ya faru ne a ranar Juma’a da yamma bayan arangama tsakanin sojoji da ‘yan bindigar.

    • Harin Ƴan Bindiga A Zamfara: Gwamna Lawal Ya Jagoranci Taron Gaggawa Kan Tsaro
    • Shettima Ya Yi Alƙawarin Zafafa  Yaƙi Da Ta’addanci A Arewa-Maso-Gabas

    Rahotanni sun ce tun da farko ‘yan bindigar sun fito ne daga Jihar Zamfara, inda suka kai hari ƙauyen Alhazawa da ke ƙaramar hukumar Danmusa a ranar Alhamis domin satar shanu.

    Sai dai mazauna ƙauyen sun yi ƙoƙarin kare kansu, inda suka kashe huɗu daga cikin ‘yan bindigar.

    Bayan kwana ɗaya, ‘yan bindigar sun sake taruwa domin su kai hari domin ɗaukar fansa kan mazauna ƙauyen.

    Amma a hanyarsu ta zuwa ƙauyen sun haɗu da sojoji, wanda aka yi musayar wuta tsakanin ɓangarorin biyu.

    Rahotanni sun ce a lokacin arangamar an kashe ‘yan bindiga 45, yayin da sojoji uku su ma suka rasa rayukansu.

    [ad_2]

    Source link

  • Matsalar tsaro ba ta ƙara ta’azzara ba a Najeriya — Bwala

    [ad_1]



    Daniel Bwala, Mai Bai Wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, shawara kan harkokin sadarwa, ya ce matsalar rashin tsaro a Najeriya ba ta ƙara tsananta ba duk da hare-haren da ake samu a wasu sassan ƙasar.

    A ’yan kwanakin nan Najeriya ta fuskanci wasu hare-hare da suka haɗa da sace mutane da kuma kai wa wasu yankuna hare-hare.

    A farkon wannan mako, ’yan ta’addan Boko Haram da ISWAP sun sace mata da yara sama da 100 a ƙauyen Ngoshe da ke Jihar Borno.

    Da yake magana yayin wata tattaunawa a tashar Al-Jazeera a shirin Head to Head da aka yi a birnin Landan, Bwala ya ce Gwamnatin Najeriya na ƙoƙarin magance matsalar tsaro da ƙasar ke fuskanta.

    “Na yarda cewa akwai matsalar rashin tsaro a Najeriya, amma cikin shekaru biyu na wannan gwamnati an samu zaman lafiya sosai. Babu wata ƙasa a duniya da ba ta da matsalar tsaro gaba ɗaya,” in ji shi.

    Ya kuma ce Najeriya na haɗin gwiwa da wasu ƙasashe domin yaƙi da ta’addanci da inganta tsaro a faɗin ƙasar.

    “Ba za mu ce matsalar rashin tsaro na ƙara tsananta ba. A matsayinmu na gwamnati, muna aiki dare da rana domin magance wannan matsalar,” in ji shi.

    Bwala ya kuma zargi wasu kafafen yaɗa labarai na ƙasashen yamma da yi wa Najeriya da Afirka baƙin fenti.

    Ya ƙara da cewa gwamnati ta ɗauki matakai da dama wajen yaƙi da ta’addanci, ciki har da kama wasu shugabannin ’yan ta’adda da kuma yin aiki tare da ƙasashen waje domin ƙarfafa tsaro.


    [ad_2]

    Source link

  • Harin Ƴan Bindiga A Zamfara: Gwamna Lawal Ya Jagoranci Taron Gaggawa Kan Tsaro

    [ad_1]

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jajanta wa al’ummomi da iyalan waɗanda hare-haren ’yan bindiga suka shafa a sassa daban-daban na jihar, yana mai tabbatar da ƙudurin gwamnatinsa na kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta daɗe tana addabar yankin.

    Gwamnan Lawal ya kira tare da jagorantar wani taron gaggawa na Majalisar Tsaron Jihar a ɗakin taro na Gidan Gwamnati da ke Gusau.

    • Kiwon Awakan Alfarma Na Ƙara Haɓaka A Jihar Kano
    • Rigakafin Cutar Shanyewar Barin Jiki

    Taron ya haɗa shugabannin hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki domin duba halin da ake ciki da kuma ɗaukar matakan gaggawa.

    A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an bayyana cewa kiran taron ya biyo bayan rahotanni masu tayar da hankali, musamman sahihan bayanai kan zargin dasa bama-bamai na na’urorin fashewa (IED) a kan wasu manyan hanyoyin jihar.

    Sanarwar ta ce, gwamnan ya umarci shugabannin hukumomin tsaro da su sake nazari kan tsarin tsaron da ake da shi a halin yanzu, tare da samar da ingantaccen tsari na aiki mai ma’ana, tsari da haɗin gwiwa domin daƙile wannan sabon salo na barazana.

    “Taron ya nuna haɗin kai da ɗaukar alhakin bai ɗaya tsakanin gwamnatin jihar da hukumomin tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Zamfara,” in ji sanarwar.

    Gwamna Lawal ya buƙaci hukumomin tsaro da su ƙara ƙaimi wajen tattara bayanan sirri, ƙara sanya ido da ɗaukar matakan haɗin gwiwa cikin gaggawa domin hana miyagun mutane ƙara samun galaba.

    Ya jaddada muhimmancin kasancewa a gaba da masu aikata laifi, tare da taƙaita musu damar motsi da murƙushe duk wata barazana ba tare da jinkiri ba.

    Bugu da ƙari, gwamnan ya miƙa saƙon ta’aziyya ga hukumomin tsaro bisa rasuwar jami’ansu da suka sadaukar da rayukansu wajen kare al’umma, tare da yi wa waɗanda suka jikkata fatan samun sauƙi cikin gaggawa.

    Haka kuma, ya jajanta wa iyalan waɗanda suka rasa rayukansu da al’ummomin da hare-haren suka shafa, yana mai tabbatar da cewa gwamnati za ta ba da cikakken goyon baya na kayan aiki, dabaru da tsari domin ƙara ƙarfin hukumomin tsaro.

    Gwamnatin Zamfara ta jaddada cewa za ta ci gaba da saukar dukkan matakan da suka dace domin dawo da zaman lafiya mai ɗorewa a faɗin jihar, tare da tabbatar da cewa tsaro ya zama ginshiƙin ci gaban al’umma.

    [ad_2]

    Source link

  • Farashin fetur ya kai N1,080 kan kowace lita a Legas

    [ad_1]



    Farashin Litar Man Fetur ya ƙaru zuwa Naira 1,080 a wasu sassan Jihar Legas, sakamakon tashin ɗanyen mai a kasuwar duniya.

    Bincike ya nuna wasu gidajen mai a ranar Asabar sun fara sayar da man tsakanin Naira 1,020 zuwa Naira 1,080 kan kowace lita.

    Ƙarin farashin ya biyo bayan ƙara kuɗin mai da matatar Dangote ta yi.

    Farashin ya shafi masu ɗauko mai kai-tsaye daga matatar mai kafin su sayar wa jama’a.

    Rahotanni sun ce matatar ta ƙara farashin zuwa Naira 995 kan kowace lita daga Naira 874, saboda tashin farashin ɗanyen mai a kasuwar duniya.

    A yanzu haka ana sayar da gangar ɗanyen mai kusan dala 92.69 kan kowace ganga.

    Farashin ɗanyen mai ya ƙaru ne saboda rikicin da ya ɓarke a yankin Gabas ta Tsakiya.

    Masana harkar makamashi sun ce rikicin da ya shafi Amurka, Isra’ila da Iran na iya shafar samar da ɗanyen mai a duniya, wanda zai iya ƙara tashin farashin mai.

    Masana sun kuma yi gargaɗin cewa idan farashin ɗanyen mai ya ci gaba da ƙaruwa, farashin man fetur a Najeriya na iya tashi har ya kai kusan Naira 1,100 kan kowace lita.

    Bincike ya nuna cewa gidajen mai da dama sun riga sun ƙara farashin nasu.

    A halin yanzu kuma, rahotanni daga Ibadan sun nuna cewa a wasu wurare ana sayar da man fetur a kan Naira 1,200 kan kowace lita.


    [ad_2]

    Source link

  • Ta’addanci Ya Sa Fiye Da Mutun 300,000 Rasa Matsuguni A Neja – Bago

    [ad_1]

    Gwamnan Jihar Neja, Umaru Mohammed Bago, ya bayyana cewar fiye da mutane 300,000 suka rasa wuraren zamansu a ƙannan hukumomi goma na Jihar saboda ci gaba da taɓarɓarewar tsaro da aka daɗe ana fama da shi, a Jihar.

    Neja tana daga cikin Jihohin da lamarin ta’addanci na rashin tsaro yayi ma katutu, inda ƙungiyoyin ƴan ta’adda lokaci zuwa lokaci suna zuwa wuraren zama mutane da basu ji basu gani ba, suna karkashe mutane da garkuwa dasu,da suka haɗa da yara ƴanmakaranta.

    Gwamna Bago Ya Gargadi ‘Yan APC Masu Yi Wa Jam’iyyar Zagon Kasa

    Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihohin Makwabta, Ya Kara Ta’azzarar Rashin Tsaro A Neja – Bago

    Hare- haren ya kawo cikas ga yadda mutane suke suke neman yadda za su tafiyar da rayuwarsu, ya sa mutane da yawa yin ƙaura, hakan ya ƙara tsaurara rashin tsaro a ƙauyuka.

    Sanadiyar hakan, iyalai da yawa yanzu suna zama cikin yanayin tsoro.An ƙauracewa gonaki saboda barazanar tashin hankalin, yayin da su kuma iyaye suka ƙagara su tura ‘ya’yansu zuwa makaranta.

    Halin kai hare- haren ba kawai lamarin aikin noma ya shafa kaɗai ba, har ma da matsalolin raba kayan agaji a Jihar.

    Da yake yi ma ƴanjarida jawabi ranar Asabar a Minna bayan da ya amshi kayan jinƙai daga gwamnatiun tarayya, Gwamna Bago ya bayyana yawan mutanen da suka rasa matsuguni a sanadiyar ci gaban da ake yi na kai farmaki a ƙananan hukumomin da abin ya shafata.

    Ya ce“a yanzu, muma iya bada ƙiyasin, muna da fiye da mutane 300,000 da suka rasa wuraren zama a ƙananan hukumomi goma da abin ya shafa a faɗin Jihar Neja waɗanda suke fama da lamarin tsarin daya shafi tsaro,”.

    Gwamnan ya ƙara da cewa gwamnatin sa tana aiki da tuntuɓar gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro, saboda a samu damar dawo da zaman lafiya a wuraren da matsalolin suka fi shafa.

    Ya bada tabbacin cewar yayin da hukumomin tsaro suka kawo taimako hakan zai sa waɗanda suka rasa wuraren zamansu su koma gidajensu domin ci gaba da rayuwa kamar yadda suka saba.

    [ad_2]

    Source link

  • Shettima Ya Yi Alƙawarin Zafafa  Yaƙi Da Ta’addanci A Arewa-Maso-Gabas

    [ad_1]

    Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya yi alƙawarin cewa Gwamnatin Tarayya za ta kawo ƙarshen ta’addanci a yankin Arewa-Maso-Gabas ta hanyar “karfafa ƙarfin Soji,” biyo bayan wasu hare-hare masu muni da aka kai a Jihar Borno.

    A cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Asabar ta hannun Babban Mataimakinsa na Musamman kan Harkokin Sadarwa da Kafofin Watsa Labarai, Stanley Nkwocha, Shettima ya ce gwamnati ba za ta bar fargaba ta sanya ta dakatar da aiki ba, duk da satar mutane a Ngoshe da hare-haren da aka kai kan rundunonin Soja.

    • Tinubu Ya Tura Kashim Shettima Kano, Ya Yi Alƙawarin Tallafin Kuɗi Ga Ƴan Kasuwar Singa
    • 2027: Tinubu Ya Jaddada Shirin Tafiyarsa Tare Da Shettima

    “Muna ɗaya daga kasa cikin ƙasashe da suke fama matsalar tsaro. Mutuncin rayuwar ɗan adam ba abin sassauci ba ne. Wannan rashin imanin da suke zai kawo ƙarshe, ba da magana kawai ba, amma da ƙarfin hukuma,” in ji shi.

    Shettima ya bayyana cewa ana ƙara tura kayan aiki na dabaru da ƙarin Sojoji bisa bayanan sirri zuwa wuraren da abin ya shafa. Ya ce Shugaba Bola Tinubu ya samu rahoto kan lamarin kuma ya umarci “ayi gaggawar tura dukkanin matakan samar da tsaro.”

    Ya ƙara da cewa gwamnati ba za ta lamunci barin wata mafaka ga waɗanda ke neman tilasta wa mutane barin gidajensu ko mamaye wani wuri a Nijeriya ba. Shettima ya yi alƙawarin cewa waɗanda suka aikata laifukan za su fuskanci hukunci bisa doka, sannan waɗanda aka sace za a mayar da su gida cikin aminci ga iyalansu.

    Mataimakin Shugaban ƙasar ya yi godiya ga jajircewar mazauna Jihar Borno ƙarƙashin gwamna Babagana Zulum da kuma jaruntakar Sojojin da ke fagen daga. Shugaba Bola Tinubu kuma ya nuna tausayawa da goyon baya ga gwamnan yayin da ya kira shi kan hare-haren, yana mai tabbatarwa cewa Nijeriya za ta ci gaba da samun nasara kan ta’addanci.

    [ad_2]

    Source link

  • Iran ta nemi afuwar maƙwabtan ƙasashe ta gindaya sharaɗin daina kai musu hari

    [ad_1]



    Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian ya ce sun dakatar da kai hari ƙasashen da ke maƙwabtaka da su bisa sharaɗin Amurka ba za ta yi amfani da ƙasashen wajen kai masu hari ba.

    Wannan na cikin wani jawabi da kafafen yaɗa labarai na Iran suka wallafa a ranar Asabar, inda kuma shugaban ya bayar da haƙuri ga ƙasashen kan hare-haren da suka faru a kwanakin baya tun bayan fara yaƙi tsakanin ƙasar da Amurka da kuma Isra’ila.

    A cikin wani saƙon bidiyo da aka yaɗa ta gidan talbijin na ƙasar, Mista Pezeshkian ya ce “ya zama wajibi mu nemi wannan afuwa na ƙasashen da muka kai wa hari.

    “Ba mu da niyyar far wa maƙawambtanmu.”

    Pezeshkian ya ƙara da cewa gwamnatin ƙasar ta bai wa sojojin ƙasar umarnin “daga yanzu kada a sake kai wa wata ƙasa maƙwabciyarmu hari, in ba ita ta fara kawo mana harin ba.

    “Ga waɗanda ke tunanin za su yi amfani da wannan lokaci da muke ciki don kai wa Iran hari, su sani ba za mu ƙyale ba, kuma goyon bayan Isra’ila ko Amurka ba hanya ce ta girmama ’yanci ba,” in ji shi.

    Tun dai bayan da Isra’ila da Amurka suka ƙaddamar da hare-hare kan Iran tare da kashe jagoran addinin ƙasar, Ayatollah Ali Khamenei, Iran ta mayar da martani ta hanyar ƙaddamar da hare-hare kan sansanonin sojin Amurka da ke yankin Gabas ta Tsakiya.


    [ad_2]

    Source link

  • Rashin Tsaro Yayi Sauƙi A Mulkin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu – Daniel Bwala

    [ad_1]

    Mai Ba Shugaban Kasa Shawara Kan Huldar Manufofin gwamnati, Daniel Bwala, ya ce matsalar rashin tsaro a Nijeriya bai kara ta’azzara ba, inda ya jaddada cewa Gwamnatin Tarayya na ɗaukar matakai na dindindin don rage tasirin matsalar.

    Bwala ya bayyana hakan ne a shirin Head to Head na Al Jazeera, da Mehdi Hasan ke gabatarwa a Conway Hall, wanda aka wallafa ranar Juma’a ta kafafen sada zumunta na shirin. Ya amince cewa rashin tsaro yana nan, amma ya ce ba a samu taɓarɓarewar yanayi ba a ƙarƙashin gwamnatin yanzu. Ya kuma bayyana cewa babu ƙasar da ke cikakken tsaro, inda ya kawo wasu sassan London a matsayin misali.

    • Yaƙin Iran: Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Matakan Tsaro A Yankin Gabas
    • Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

    Bwala ya ƙara da cewa gwamnatin Tinubu na aiki tare da ƙasashen duniya wajen yaƙi da ta’addanci, inda ya ambaci tafiyar Shugaba Bola Tinubu zuwa Turkey da haɗin gwuiwa da Amurka, tare da sanar da cewa an kama shugabannin Boko Haram da Lakurawa watanni shida kafin maganganun Donald Trump. Game da ƙaruwar satar mutane, ya bayyana hakan da matsalar a matsayin “tattalin arziƙin” amma ya tabbatar da cewa gwamnati na ɗaukar matakai don magance ta.

    Ya kuma bayyana cewa shirin Safe Schools Initiative yana taimakawa wajen kwashe ɗalibai daga wuraren da rashin tsaro ya fi yawa zuwa biranen jihar masu tsaro, don tabbatar da samun damar karatu lafiya.

    [ad_2]

    Source link

  • Babu Tabbacin Za Mu Iya Gudanar Da Sahihin Zaɓe A 2027 —Shugaban INEC

    [ad_1]

    Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC), Farfesa Joash Ojo Amupitan, ya ce babu tabbacin ko hukumar zaɓe za ta iya gudanar da sahihin zaɓe mai cike da nasara 100 bisa 100 a 2027 ko da ta saka sakamakon zaɓen a na’ura.

    Amupitan ya bayyana hakan ne a yayin wani taro da ƙungiyar farar hula ta mai neman a inganta harkokin zaɓe ta shirya, wanda aka gudanar a Otel ɗin Abuja Continental, a ranar Lahadi da ta gabata.

    A cewarsa, zaɓen shugaban ƙasa na 2027 zai kasance mafi kyau a tarihin Nijeriya.

    Ƙungiyoyin farar hula da masana harkokin zaɓe da masu sa ido a cikin harkokin zaɓe da kuma wakilan al’umma na daga cikin waɗanda suka halarci a taron don tattauna al’amuran da suka shafi zaɓe.

    • Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe
    • Majalisar Ƙoli Kan Shari’ar Musulunci Ta Sake Neman A Cire Shugaban INEC

    Sai dai kuma Amupitan ya ce Nijeriya na buƙatar yin amfani da sauƙaƙan dokar harshe, inda zai yi saukin fahimta ga kowane ɗan Nijeriya tare da yaba wa kowane sashe na dokar zaɓe ta 2026.

    Ya ce a yayin zaɓen shugabannin ƙananan hukumomin Abuja, sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi biyar an bayyanasu a kan lokaci, amma sakamakon zaɓe ƙaramar hukumar Kuje bai bayyana kan lokaci ba har sai da ya kai rana ta gaba.

    Amupitan ya ƙara da cewa ya kamata a tabbatar da cewa zaɓe mai nasara ya dogara ne kan kammala tsarin kayan aiki.

    Amupitan ya ce, “Na farko, idan kana son auna ko zaɓen ya yi nasara, dole ne ka tantance ko an fara zaɓen kamar yadda aka sanar. Kuma mun sanar da zaɓen da ƙarfe 8.30. Don haka idan mun iya fara zaɓen da ƙarfe 8.30 shi ne za mu iya samun nasara.

    “Na biyu, idan zaɓen ya kasance cikin lumana. Na uku, idan muka iya sarrafa sakamakon zaɓen yadda ya kamata, sannan a bayyanar da sakamakon, to za ka iya cewa ka yi zaɓe mai nasara.

    “A matsayinmu na hukumar da ke sa ido, mun ƙudiri aniyar cimma duk wannan nasarar.

    “Amma duk da haka, dole mu yarda cewa akwai wasu matsalolin kayan aiki, wasu kuwa na Ɗan’adam ne, kuma muna ƙoƙarin magancesu. Bari in roƙi ‘yan Nijeriya, saboda na lura yanzu cewa abin da ‘yan Nijeriya suke so shi ne, sahihin zaɓe. Zan yi ƙoƙarina daidai gwargwadon ikona don ba wannan ƙasa zaɓe mafi kyau.

    “Watakila ba za mu iya samun zaɓen kashi 100 cikakke a yanzu ba. Amma dangane da isar da sakamakon ta hanyar na’ura, na riga na faɗa a gabanin zaɓen shugabannin ƙananan hukumomin Abuja cewa muna da ikon isar da sakamakon ta na’ura, kuma za mu sanar da sakamakon ta na’ura.

    “Abin da kawai ke damunmu shi ne, lokaci na haƙiƙa. Mene ne lokaci na haƙiƙa? Misali, idan ka tafi, ka yi amfani da manhajarka don tura kuɗi daga asusunka. Ko a cikin birnin Abuja, ka tura naira 50,000 zuwa ga Mista B, kuma daga manhajarka, kuɗin ya tafi.

    “Amma mutumin bai ga kuɗin ba har sai bayan wasu mintuna 30, wani sa’a, ko ma da yamma. Don haka waɗannan wasu ne daga cikin abubuwan. Kuma lokacin da ka ce lokaci ne na haƙiƙa, da zarar an gama, dole ne a karɓa.

    “Saboda haka, gudanar da sakamakon zaɓe da kayan aiki su ne manyan batutuwa guda biyu da, daga ɓangarenmu, muna ƙoƙarin ganin yadda za mu iya gudanar da su sosai, domin inganta gaskiya da amincin tsarin.

    “An kawar da matsalar na’ura. Na’ura ba zai sake kawo matsala ba a zaɓen Nijeriya, kuma duk lokacin da na kalli sashe na 63 na dokar zaɓe, ko a zaɓen ƙananan hukumomin abuja, ban da wannan jinkiri, ba mu samu wata matsala ta na’ura ba, ma’ana cewa kwai an samar da ita ne don kariya. Kuma a lokacin mulkina, ba za ta gaza ba.

    “Ko da ta gaza, dole ne a sanar da sakamakon zaɓe. Amma matsalar kaɗai ita ce, idan ta gaza sanar da sakamakon zaɓe a kan lokaci, kamar yadda muka samu a wancan ƙaramar hukuma.

    “Wannan shi ne babban matsala. Yanzu da haka da nake yin magana game da magance matsalar, zaɓe yanzu, ko da yaushe, yana da nasaba da fasaha. Amma kafin ka yi amfani da kowace fasaha, yana da muhimmanci ka gwada wannan fasaha sosai.

    “Don haka bincikena na zaɓen 2023 shi ne yayin da aka gwada na’urar a cikin jihohi, alal misali zaɓɓen Osun, zaɓen Ekiti, duk da haka, lokacin da ya zo ga zaɓen tarayya, musamman zaɓen shugaban ƙasa wanda yanzu ya zama na tsakanin jihohi, ba a gwada shi yadda ya kamata ba.

    “Don haka, ɗaya daga cikin abubuwan da muke ƙoƙarin yi kafin zaɓen shi ne, tabbatar da cewa an sanar da sakamakon zaɓen ta na’ura a dukkan faɗin jihohin ƙasar nan.

    “Da yardar Allah, zaɓen shekarar 2027 zai kasance mafi kyawun zaɓen da ‘yan Nijeriya za su yi. Domin ‘yan Nijeriya a 2023 sun sha bamban da abin da za ku samu a 2027. Mutane sun ƙara samun wayewa sosai.”

    [ad_2]

    Source link

  • Kiwon Awakan Alfarma Na Ƙara Haɓaka A Jihar Kano

    [ad_1]

    Kiwon Awakai na cikin gida, musamman a Jihar Kano ya fara fusknatar ƙalubale, musamman saboda yadda wasu a ƙauyukan jihar, suka fara raja’a wajen fara kiwon wasu nau’ikan Awaki da aka fi sani da na alfarama.

    Kusan za a iya cewa, a ɗaukacin wasu ƙauyukan da ke jihar ta Kano, kiwon Shanu na ɗaya daga cikin fannin da ya yi fice a jihar, duba da cewa; ana samun kuɗaɗen shiga da samar da wadataccen abinci da kuma inganta rayuwar masu kiwonsu.

    • Bukukuwan Ƙarshen Shekara: NSCDC Ta Tura Jami’anta 4,000 Don Tsaro A FCT
    • Abubuwan Da Ya Kamata A Lura Da Su Kafin Fara Kiwon Agwagwa (Geese)

    Sai dai, a yanzu fannin kiwon Akuyoyin na alfarama a ƙauyukan jihar, za a iya cewa; ya shiga gaban kiwon na Shanu, musamman duba da cewa; wasu nau’ikan Akuyoyin da ake shigowa da su cikin ƙasar, wasu masu kiwon, sun mayar da hankali wajen kiwata su, musamman domin su sama wa kansu kuɗaɗen shiga masu yawa.

    An shafe shekaru ana kiwon Akuyoyi a ƙasar nan, waɗanda akasari ana kiwata su ne, domin cin namansu a gida.

    Amma sai dai a yau, akwai wasu nau’ikan na Akuyoyi na daban da aka fi mayar da hankali wajen kiwata su, musamman kamar irin nau’ikan Saanen, Damascus da kuma Gulabi waɗanda kuma sun rungumi kiwonsu ne, domin samar da kuɗaɗen shiga.

    Akasarin waɗannan nau’ikan na Akuyoyi, masu kuɗi ne suka fi sayen su, domin kiwata su da kuma wasu masu sha’awar yin kiwo.

    Ɗaya daga cikin masu kiwata irin waɗannan Akuyoyi, wanda kuma ya kasance ɗaya a kan gaba wajen rungumar kiwata su, mai suna Malam Sunusi Ali Musa, da ke Jihar Kano ya bayyana cewa; kwatsam ya tsinci kansa a cikin sana’ar fara kiwata wannan nau’i na Akuyoyi.

    “Mun fara kiwata su ne, a bisa sha’awa kawai, daga baya sai muka lura jama’a sun fara nuna ra’ayinsu na kiwata su, inda ya ƙara da cewa; irin waɗannan Akuyoyin na alfarma, ana kiwata su ne domin kasuwanci a babban mataki” in ji shi.

    A cewarsa, ya fara zuba jarin da a kiwata nau’in Saanen, a waɗanda ana shigo da su ne daga Gabas ta Tsakiya, kuma ana samun nono a jikinsu mai yawan gaske.

    Ya ƙara da cewa, wasu na sayen nononsu, domin sarrafa shi zuwa magunguna, inda kuma wasu ke kiwata irin waɗannan Akuyoyi domin ado a gida.

    Shi ma wani wanda ya rungumi irin wannan kiwo, mai suna Malam Isma’ila Ahmad, a yanzu nau’in Akuyar na Damascus, shi ne ya fi yin tashe kuma suna samar da ingantaccen nama.

    Kazalika, Ahmad ya kuma bayyana wani nau’in Akuwar wanda ake kira da Gulabi, kuma akasarinsu farare ne da aka shigo da su daga ƙasar Pakistan.

    Samun irin waɗannan nau’ikan na Akuya, ba abu ne mai sauƙi ba, kuma akasarinsu ana safarar su ne daga ƙasashe kamar irin su Libiya da Jamhuriyar Nijar.

    An ruwaito cewa, nau’in Akuya na Damascus ana sayar da su ne a kan naira miliyan 3.5, inda kuma nau’in Gulabi ake sayar da su a kan naira miliyan 3 .

    Wasu daga cikin masu sana’ar, Alhaji Usman Baba Gara, ya bayyana cewa; kiwon irin waɗannan Akuyoyin a Jihar Kano, na ƙara tumbatsa, musamman ganin cewa, ana samun riba mai yawa, wanda hakan ya sanya ake ƙara samun wasu masu son shiga fannin kiwon nasu.

    Sai dai, ya yi gargaɗin cewa; dole ne ga duk mai son kiwata su ya tabbatar da yana bin ƙa’aida, musamman domin kare su daga kamuwa da cututtuka daban-daban.

    Bugu da ƙari, su ma wasu ƙwararrun likitocin dabbobi a jihar, sun tabbatar da hakan, inda suka sanar da cewa; irin waɗannan Akuyoyin na alfarma, suna buƙatar son kulawa matuƙa da gaske.

    [ad_2]

    Source link