CAF Tayi Watsi Da Alƙalan Wasan Nijeriya a Kofin Afrika Na 2025
[ad_1]
Hukumar ƙwallon ƙafa ta Nahiyyar Afrika (CAF) ta fitar da jerin alƙalan wasa da masu kula da na’urar VAR a gasar cin kofin Nahiyyar Afrika ta 2025, amma babu ɗan Najeriya ko ɗaya.
A sanarwar da hukumar ta fitar, ta ayyana alƙalan wasa 28 da masu kula da VAR 14 daga ƙasashe daban-daban.
Hukumar ta zaɓo alƙalan wasa biyu daga ƙasashen Maroko, Aljeriya, Masar, da kuma Mauritaniya.
Masana harkokin wasanni dai na ganin cewa matsalar cin hanci da rashawa ne dalilin yin shagulacin ɓangaro ga alƙalan wasan Najeriya, saboda karɓar na goro musamman a gasar Firimiya.
Kawo yanzu an shafe shekaru 19 rabon da wani alƙalin wasa daga Najeriya ya busa gasar cin kofin Nahiyyar Afrika.
Za a fara gasar daga ranar 21 ga watan Disamba 2025 zuwa 18 ga watan Janairun 2026.
Ƙasar Maroko ce za ta buɗe gasar da karɓar baƙuncin Comoros a birnin Rabat.
Mai dangantaka
[ad_2]
Source link