Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba

[ad_1]

Shugaba Bola Tinubu a ranar Litinin ya gargadi jami’an shari’a a fadin kasar cewa dole ne a tabbatar da adalci ga kowa – Talaka da mai kudi, ba tare da nuna wata wariya ba, ko karɓar cin hanci, “bai dace adalci ya zama na sayarwa ba.”

Da yake jawabi a yayin bude taron alkalan Nijeriya na kotunan koli na shekarar 2025 a Abuja, Tinubu ya jaddada cewa jami’an shari’a su ne ainihin masu kula da adalci, don haka, shugaban ya tabbatar da goyon bayansa kan samar da walwala, horo, da inganta Cibiyar Shari’a ta Kasa.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *