Ba rashin tsaro ba ne matsalar najeriya —Farfesa Okolo

[ad_1]



Matsalar Najeriya ba ta tsaro ba ce, illa rashin kyakkyawan shugabanci, a cewar Farfesa Philips O. Okolo, Farfesa a fannin Ci gaba, Zaman Lafiya da Nazarin Tsaro a Jami’ar Yankin Neja Delta (NDU), Amassoma.

Da yake gabatar da jawabi a taron jami’ar mai taken “Cin Hanci, Shugabanci da Ci gaba: Najeriya tana da Tsaro,” Farfesa Okolo ya ce rashin ingantaccen shugabanci ne tushen cin hanci da durƙushewar ci gaban ƙasa.

Ya bayyana cewa shugabanci na nufin yadda ake yanke shawara, yadda ake amfani da iko da yadda cibiyoyi ke aiki, tare da ginshiƙai irin su gaskiya, riƙon amana, shiga tsakanin jama’a da adalci.

Farfesan ya ce nau’o’in cin hanci da suka haɗa da na ƙananan jami’ai, wanda ake aikatawa a kullum; na manya wanda ya yi katutu a tsarin rayuwa; na siyasa ta hanyar karkatar da manufofi da ƙa’idoji; da kuma na ofisoshi wanda ke faruwa a ma’aikatun gwamnati.

“Tsaro ba wai matakan soja kawai ba ne,” in ji shi. “Tsaro yana nufin samun damar tattalin arziki, adalci, dogaro da cibiyoyin gwamnati, da rayuwa ba tare da tsoro ba. Idan babu shugabanci nagari, waɗannan duka ba za su tabbata ba.”

Ya buƙaci shugabannin ƙasa su samar da manufofin da za su ƙarfafa matasa don cimma burinsu, yana mai bayyana matasan a matsayin masu juriya, ƙwazo, da fasaha ta zamani.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *