APC Ta Shirya Karɓar Gwamna Yusuf — Abdullahi Abbas
[ad_1]
Jam’iyyar APC a Jihar Kano ta ce ta shirya karɓar Gwamna Abba Kabir Yusuf cikin jam’iyyar kafin ficewar sa daga Jam’iyyar NNPP.
Shugaban APC na Kano, Yarima Abdullahi Abbas, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, 29 ga Disamba, 2025.
A cewar Abbas, an ɗauki wannan matakin ne don samar da haɗin kai da sulhu a Jihar Kano.
“Wannan matakin yana nufin hadin kai, sulhu da ciyar da Jihar Kano gaba,” in ji shi.
Abbas, wanda ke magana a madadin tsohon shugaban jam’iyyar na kasa kuma tsohon gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce APC ta shirya tarbar Yusuf da sauran mambobin NNPP a hukumance, ciki har da ‘yan majalisa, ‘yan majalisar zartarwa na jiha, shugabannin ƙananan hukumomi, kansiloli da kuma wadanda ke riƙe da muƙaman siyasa.
Ya kara da cewa, za a gudanar da liyafar da aka shirya “cikin yanayi na girmama juna da mutuntawa.”
[ad_2]
Source link