An sallami Kwamishinar Mata ta Jihar Bauchi daga aiki
[ad_1]
Gwamna Bala Abdulkadir Mohammed na Jihar Bauchi, ya sallami Kwamishinar Harkokin Mata da Ci-gaban Yara, Zainab Baban Tanko.
Sanarwar da kakakin gwamnan, Mukhtar Giɗaɗo, ya fitar ta bayyana cewa sallamar ta fara aiki ne nan take.
Ya bayyana cewa hakan ta faru ne a sakamakon sauye-sauye a majalisar zartarwa ta Jihar Bauchi.
Ya bayyana godiyar Gwamna Bala ga tsohuwar Kwamishinar bisa gudummawar da ta bayar ga ci-gaban jihar, tare da yi ,ta fatan alheri.
Mai dangantaka
[ad_2]
Source link