An kashe ‘Yan Ƙasarmu 32 A Lokacin Mamayar Amurka A Venezuela — Gwamnatin Cuba
Gwamnatin Cuba a ranar Lahadi ta yi iƙirarin cewa ‘yan ƙasarta 32 sun mutu a lokacin wani farmakin da Amurka ta kai a Venezuela da nufin kama Shugaba Nicolás Maduro domin fuskantar shari’a a Amurka.
Gwamnatin Cuba ta sanar da ware kwanaki biyu na zaman makoki na ƙasa a ranakun 5 da 6 ga Janairu don girmama waɗanda aka kashe, ta ƙara da cewa za a fitar da cikakkun bayanai game da shirye-shiryen jana’iza daga baya.
- Da Ɗumi-ɗumi: Manchester United Ta Sanar Da Korar Kocinta Ruben Amorim
- ‘Yan Sama Jannatin Sin Sun Yi Nasarar Kammala Horon Farko Cikin Kogo
“Sun tsaya da gaske kan sauke nauyin da ke kansu game da tsaro, sun rasu cikin mutunci da jarumtaka, bayan turjiya mai tsanani, har maharan suka kai musu hare-haren bama-bamai a shingayensu,” in ji sanarwar.
Gwamnatin Cuba ta daɗe tana ba wa Maduro tallafin tsaro tun lokacin da ya hau mulki, amma har yanzu ba a san adadin ma’aikatan Cuba da ke gadin shugaban Venezuela a lokacin hare-haren ba a wurare daban-daban.
Sojojin Amurka sun kama Maduro, mai shekaru 63, da matarsa, Cilia Flores, a Caracas ranar Asabar, sannan suka kai shi Amurka, inda a halin yanzu ake tsare da shi a wani gidan yari da ke New York kafin a fara shari’arsa a ranar Litinin bisa zarginsa da safarar miyagun kwayoyi.