Amurka za ta turo sojojinta 200 Najeriya
[ad_1]
Ƙasar Amurka za ta turo kusan sojojinta 200 zuwa Najeriya domin horas da rundunar sojin ƙasar a yaƙin da take yi da ’yan ta’adda.
Jaridar Jaridar Wall Street ta ƙasar Amurka ce ta wallafa wannan rahoton a ranar Talata.
Ta ce wani jami’in sojin Amurka ya shaida wa jaridar cewa wannan mataki ya biyo bayan makonni bayan Shugaban Ƙasar Donald Trump ya zargi Najeriya da gazawa wajen kare Kiristoci daga hare-haren ’yan ta’adda.
Rahoton ya ce sojojin za su ƙarfafa ƙarfin Najeriya wajen yaƙi da ta’addanci ta hanyar horaswa da tallafin aiki.
Bugu da ƙari, sabbin jami’an da za a tura za su taimaka wa sojojin cikin gida da bayanan sirri don gano wuraren kai hare-hare.
A yayin wani taron bayani ta yanar gizo a makon da ya gabata, kwamandan rundunar Amurka a kasashen Afrika, (USAFRICOM), Janar Dagvin R. Anderson, ya tabbatar da ƙaruwa a haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen biyu bayan tattaunawa a matakin shugabanni.
Ya ce: “Na samu damar ganawa da Shugaba Tinubu. Mun tattauna kuma mun amince cewa dole ne mu yi aiki tare wajen nemo mafita a yankin.
“Wannan ya haifar da ƙaruwa a haɗin gwiwa, ciki har da ƙaramar tawagar Amurka da ke kawo ƙwarewa ta musamman domin ƙara ƙarfin abin da Najeriya ta dade tana yi.”
Hedikwatar Tsaro ta Najeriya ta bayyana cewa haɗin gwiwar tsaro da Amurka za ta fi karkata kan gina ƙwarewa, ba yaƙin kai tsaye ba.
A cewar rundunar, haɗin gwiwar ta haɗa da horar da sojoji, musayar bayanan sirri, tallafin kayan aiki da tattaunawar dabaru domin magance matsalolin tsaro da ake fuskanta, musamman ta’addanci.
Wannan bayani ya biyo bayan rahotanni a kafafen yaɗa labarai da kuma hasashe daga jama’a kan tura sojojin Amurka a Najeriya.
A cikin wata sanarwa, Daraktan Yaɗa Labarai na rundunar, Manjo Janar Samaila Uba, ya ce dukkan haɗin gwiwa da Amurka ana gudanar da su ne cikin girmama ikon Najeriya da kuma tsarin da aka kafa na haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen biyu.
Sanarwar ta ce: “Hedikwatar Tsaro ta lura da rahotannin kafafen yaɗa labarai da hasashen jama’a kan kasancewar ko tura sojojin Amurka a Najeriya.
“Rundunar Sojin Najeriya tana so ta bayyana cewa Najeriya tana da doguwar haɗin gwiwa ta tsaro da Amurka.”
Haka kuma, Shugaba Tinubu a ranar Lahadi ya karɓi tawagar manyan jami’an Amurka ƙarƙashin jagorancin kwamandan USAFRICOM a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.
Masu alaƙa
[ad_2]
Source link