Ambaliya: NEMA ta raba kayan tallafi a Yobe

[ad_1]



Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), ta raba wa mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Ƙaramar Hukumar Potiskum ta Jihar Yobe, kayan tallafi.

Darakta Janar na hukumar, Zubaida Umar, ta amince da fara wannan tallafi a Potiskum, inda ta samu wakilcin Abdullahi Garba, ko’odinetan ofishin NEMA na Maiduguri.

A cewarta, wannan mataki ya biyo bayan ambaliyar ruwa da ta auku a ranar 15 ga qatan Agusta, 2025.

Ambaliyar ta shafi dubban jama’a kuma ta lalata gidaje da dama.

Binciken da NEMA tare da wasu ƙungiyoyin agaji suka gudanar ya nuna cewa gidaje 2,557 ne abin ya shaf, inda wasu suka rushe baki ɗaya.

Wuraren da ambaliyar ta fi shafa sun haɗa da tsohon gidan yari, Filin Mashe, Unguwar Makafi, Unguwar Jaje, Tsangaya, Rugan Fulani, da Bayan Sabon Gidan Yari.

Zubaida, ta bayyana cewa rabon kayan agaji kamar abinci, kayan masarufi, da kayan gini na nufi rage wa jama’a raɗaɗin da iftila’in da ya same su.

Ta ƙara da cewa: “Wannan mataki ya nuna cewa NEMA da abokan hulɗarta suna da niyyar taimaka wa al’umma domin rage musu raɗaɗin da ya faru.”

Hukumar ta yi rabon kayan ne tare da haɗin gwiwar Hukumar Agajin Gaggawa ta Jihar Yobe (SEMA) da kuma hukumomin tsaro a jihar.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *