Akasarin masu kai mana hare-hare daga jihohin da suka kewaye mu suke – Gwamnatin Filato
Wani rahoto da kwamitin bincike da Gwamna Caleb Mutfwang ya kafa kan kashe-kashen da ke ci gaba da faruwa a Jihar Filato ya ce akasarin masu kai hare-hare suna fitowa ne daga jihohin da ke makwabtaka da Filato.
Shugaban kwamitin, Manjo Janar Rogers Ibe Nicholas, ya bayyana cewa sun gana da kabilu daban-daban da kungiyoyin masu ruwa da tsaki, tare da ziyartar dukkan al’ummomin da rikici ya shafa domin samun sahihan bayanai kan tashin hankalin da kuma hanyoyin samar da zaman lafiya mai ɗorewa.
Ya ce daga binciken da suka gudanar, an gano cewa masu kai hare-hare kan al’ummomin Filato suna fitowa ne daga jihohin Nasarawa, Kaduna, Bauchi da kuma Taraba.
“Kwamitin ya karɓi rahoton korafi daga wasu kauyuka biyu da ke jihar Nasarawa da ke iyaka da Quan’pan, inda aka ce ’yan bindiga sun kafa sansaninsu, lamarin da ya tilasta wa al’ummomin Filato da ke Quan’pan tserewa.”
“A Wase da Kanam, an samu rahoton cewa akwai sansanonin ’yan bindiga da ake zargin suna da alaƙa da kungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi.
“Dalilan da muka gano na haifar da hare-haren sun haɗa da kwace ƙasa da albarkatu faɗaɗa danniya, mamayar kabilanci da addini, rikicin siyasa, sai kuma karbar kudin fans ana masu garkuwa da mutane.
“Iyakokin da aka fi kia hari daga su sun haɗa da hanyoyin shigowa daga Nasarawa ta Wamba, Lafia da Awe; daga Kaduna ta Lere, Kaura da Sanga; daga Bauchi ta Toro, Tafawa Balewa, Bagoro da Alkaleri; da kuma daga Taraba ta Ibi da Karim Lamido.
“Wadannan hanyoyi ba sa samun kulawa sosai, kuma masu kai hari na amfani da su don kai farmaki da tserewa cikin sauri,” in ji shi.
Manjo Janar Rogers ya kuma jaddada cewa an kai hari a ƙauyuka 420, kuma kusan rayuka 12,000 sun salwanta, don haka ba za su bari a ci gaba da waɗannan kisan gillar ba.
Gwamna Caleb Mutfwang, yayin karɓar rahoton a gidan gwamnatin jihar da ke Jos, ya yi alkawarin aiwatar da shawarwarin da kwamitin ya bayar domin tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa a jihar.
Haka kuma, Gwamnan ya bayyana shirinsa na miƙa rahoton ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ƙwararrun jami’an tsaro, domin su fahimci yadda rikicin ya shafi jihar sama da shekaru 20, tare da samar da mafita mai ɗorewa.