An gano gawarwaki biyu daga gobarar gini a Legas

[ad_1]



An gano wasu maza biyu da suka mutu daga baraguzan gini mai suna Great Nigeria Insurance (GNI) da gobara ta tashi a unguwar Kasuwar Balogun da ke tsibirin Legas a jihar.

Majiyar kafar PUNCH ta ruwaito a ranar Laraba cewa gobarar ta tashi ne a hawa na huɗu inda ta bazu zuwa hawa na shida na ginin bene mai hawa 25 kafin ta ƙone sauran benaye da sauran gine-ginen da ke maƙwabtaka da shi.

Sai dai wani sashe na ginin gidan ya ruguje a lokacin gobarar, inda wasu ‘yan kasuwa suka maƙale.

Wani jami’in Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas, wanda ya zanta da manema labarai a ranar Juma’a da ya nemi a sakaya sunansa domin ba shi damar yin magana a kan lamarin, ya ce an gano gawarwakin biyu ne a ci gaba da gudanar da aikin neman waɗanda suka maƙale.

“Mun gano gawarwaki biyu a yau, an gano gawar ta farko da misalin ƙarfe 11:03 na safe, yayin da na biyun kuma da misalin ƙarfe 12:03 na rana,” in ji jami’in.

A wani bidiyo da PUNCH ta samu ya nuna yadda aka gano gawarwakin daga bisani aka sanya su cikin jakunkuna.

Duk da cewa, har yanzu ba a tabbatar da sunayen waɗanda suka mutu a hukumance ba, wani ɗan kasuwa mai suna Zacchaeus Afolayan ya ce ɗaya daga cikin su ma’aikacin kasuwa ne wanda lamarin ya rutsa da su.

“Ɗaya daga cikinsu an bayyana shi, ɗaya daga cikin yaran da ke taimaka wa ‘yan kasuwa a kasuwar, yana taimakon ‘yan kasuwa wajen kwashe kayansu a lokacin da ginin ya rufta a kansa,” in ji shi.

Duk da haka, an ci gaba da fargabar cewa, za a iya samun ƙarin ‘yan kasuwa da suka maƙale a ƙarƙashin rugujewar sashin ginin.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *