Gwamnatin Sakkwato ta bayar da umarnin biyan ma’aikata albashi

[ad_1]



Gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu ya bayar da umarnin biyan ma’aikatan jihar albashin watan Fabarairu nan take, saboda ƙaratowar watan azumin watan Ramadan.

Gwamnan wanda ya sanar da hakan ne a cikin wata sanarwa ta hannun shugaban sashen yaxa labarai da hulɗa da jama’a na ofishin gwamnan, Abubakar Bawa a yau Alhamis.

Sanarwar ta qara da cewa, matakin ya shafi: “ma’aikatan Gwamnatin jiha, ƙananan hukumomi da ma’aikatan hukumar Ilimi ta ƙananan hukumomi, da kuma tsofaffin ma’aikata masu karɓar fansho a duk faɗin jihar”.

Bayanin ya ƙara da cewa, matakin fara biyan albashin zai fara aiki ne daga ranar Juma’a 13 ga watan na Fabarairu.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *