Tsaro: An Sake Buɗe Kwalejin Jihar Kwara Bayan Rufeta A Baya

[ad_1]

An sake bude Kwalejin Ilimi ta Jihar Kwara, don ci gaba da gudanarwa bisa umarnin gwamnatin jihar duba da samun ci gaba a fannin tsaro.
Umarnin buɗewar yana ƙunshe ne a cikin wata takardar sanarwa da aka fitar a ranar Litinin kuma jaridar PUNCH ta gani.
Takardar, mai lamba: CEO/ADMIN/27/Vol.1/268, mai kwanan wata 2 ga Fabrairu, 2026, Mataimakiyar Magatakarda, Misis Lawal Taibat Saka-Bolanta ce ta sanya mata hannu.
Takardar, wacce aka aika wa ma’aikata da ɗalibai kuma aka fitar daga ofishin Magatakarda, ta bayyana cewa, kwalejin ta koma aiki nan take.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *