Kwanan nan za mu kawo karshen rikicin masarautar Kano – Gwamnati

[ad_1]



Gwamnatin jihar Kano ta ce nan ba jimawa ba za ta kawo karshen rikicin da ya daɗe yana faruwa kan masarautar Kano, inda mutum biyu ke ikirarin kasancewa halastattun sarakuna.

Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’amuran Cikin Gida na jihar, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya bayyana hakan a ranar Alhamis, inda ya ce gwamnati ta tsara abubuwa na musamman domin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a gidan sarautar.

Kusan shekaru biyu kenan Kano na fama da rikicin sarauta, inda Sarki Muhammadu Sanusi II ke zaune a fadar Gidan Rumfa, yayin da Sarki Aminu Ado Bayero ke zaune a fadar Nassarawa ƙarƙashin tsaron jami’an gwamnatin tarayya.

Yayin da yake jawabi a wani shirin na musamman a gidan rediyon Muhasa da ke Kano, Waiya ya ce sauyin shekar Gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf, zuwa jam’iyyar APC a wannan makon ce za ta kawo maslaha daga matsalar.

“Ina tabbatar muku cewa nan ba da jimawa ba, gwamnatin Kano za ta warware rikicin sarautar Kano, domin yanzu mun zama ɗaya,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa masu da’awar sarautar da kansu na iya taka rawa wajen warware rikicin, inda ya ce: “Mai yiwuwa wani ya sauka daga kujerar sarauta da kansa, ko kuma wasu su nemi sulhu saboda a samu jituwa.”

Kwamishinan ya jaddada cewa gwamnatin jihar ta kuduri aniyar tattaunawa da dukkan masu ruwa da tsaki, tare da tabbatar da cewa ba a bari lamarin ya haifar da tashin hankali ko ya kawo cikas ga mulkin jihar ba.

“Hanyar da muke bi tana kan girmama doka, sarautun gargajiya, da kuma muradun jama’ar jihar Kano,” in ji shi.

Kan sauyin jam’iyyar gwamna zuwa APC, Waiya ya bayyana matakin a matsayin ci gaban da zai kawo gagarumin alheri ga jihar.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *