An Kama Na Hannun Daman Ganduje Kan Badaƙalar ‘Dala Dry Port’ A Kano

[ad_1]

An kama Ahmad Rabiu, tsohon kwamishinan ciniki na Jihar Kano kuma tsohon daraktan tashar Dala Inland Dry Port, a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano yayin da yake shirin tashi zuwa Abuja.

Shi ne shaidar farko a shari’ar da ake yi wa Abdullahi Ganduje da wasu kan batun mallakar tashar.

  • Yadda Tayar Jirgin Sama Ta Ɓalle Bayan Tashinsa A Amurka
  • Da Pan Ji: Abincin Sinawa Da Na Fi So

Gwamnatin Kano ta ce Ganduje da abokan aikinsa sun canza hannun jarin jihar a tashar zuwa wani kamfani ba bisa ƙa’ida ba, inda aka karkatar da sama da Naira biliyan 4.49 da aka tanada don ayyukan tashar.

Akwai ‘ya’yan Ganduje da ake zargi da zama daraktoci da masu hannun jari, kuma gwamnati ta ce an yi wannan canjin ba tare da bin doka ba.

Hadiminsa ya ce an kama shi ne yayin da yake shirin zuwa Abuja.

Ganduje da sauran waɗanda ake tuhuma suna fuskantar laifuka 10, ciki har da karkatar da kuɗaɗen jama’a, cin amana da saɓa dokar mallakar dukiya.

Masu kare su sun ƙalubalanci wasu matakan kotu, bayan yin zama a bayan kan tuhume-tuhumen an ɗage shari’ar zuwa 23 ga watan Fabrairu don sauraron hujjoji na farko.

Masu gabatar da ƙara sun ce waɗanda ake tuhuma sun matsa wa wasu jami’an gwamnati da su rattaba hannu kan takardun da suka canza hannun jarin jihar na kashi 20 zuwa wani kamfani mai suna City Green Enterprise.

Sun ƙara da cewa kuɗaɗen da aka tanada don ayyukan tashar kamar hanyoyi, wutar lantarki, da katanga an yi amfani da su ne don amfanin ƙashin kai.

Gwamnatin jihar ta bayyana cewa an yi canjin ne ba bisa doka ba, kuma ta gargaɗi jami’an gwamnati kan yin amfani da muƙamansu don amfanin kansu ko na iyalansu a kan kuɗaɗen jama’a.

Ana ci gaba da bincike, kuma ana sa ran samun ƙarin wasu shaidu za su bayar da shaida a makonni masu zuwa.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *