Tinubu ya tura jakadu 4 daga cikin 68 da aka tantance

[ad_1]



Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da tura jakadu huɗu daga cikin jakadu 68 da Majalisar Dattawa ta tantance tare da amincewa da su a watan Disambar da ya gabata.

Mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara kan yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis.

A cewar sanarwar, Shugaba Tinubu ya amince da tura Ambasada Ayodele Oke a matsayin jakadan Najeriya zuwa Faransa, sai kuma Kanar Lateef Are a matsayin jakadan ƙasar zuwa Amurka.

Haka kuma, shugaban ya amince da tura Ambasada Amin Dalhatu, tsohon jakadan Najeriya a Koriya ta Kudu, a matsayin Babban Kwamishinan Najeriya zuwa Birtaniya.

Sai kuma Usman Isa Dakingari Suleiman, tsohon Gwamnan Jihar Kebbi, wanda aka tura a matsayin jakadan Najeriya zuwa Turkiyya, ƙasar da Shugaba Tinubu ke shirin kai ziyara ta musamman a mako mai zuwa.

Shugaban ya kuma umarci Ma’aikatar Harkokin Waje da ta sanar da gwamnatocin ƙasashen huɗu game da tura jakadun, kamar yadda dokokin hulɗar diflomasiyya suka tanada.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *