Sojoji sun ceto tsohon Kanar da aka sace a Filato




Sojojin Runduna Operation Enduring Peace sun ceto wani tsohon Kanar ɗin soja, Ajanaku mai ritaya, daga hannun ’yan bindiga a yankin Rafiki da ke Ƙaramar Hukumar Bassa a Jihar Filato.

Mai riƙon muƙamin Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar, Laftanar-Kanar Aliyu Danja, ya tabbatar da nasarar ceton tsohon jami’in soja.

“Ina tabbatar muku cewa dakardunmu sun ceto tsohon jami’in soja a daren jiya. Yanzu haka an kai shi cibiyar lafiyarmu domin a duba lafiyarsa,” in ji Danja.

Majiyoyi daga Bassa sun bayyana cewa ’yan bindiga sun shiga gidan Kanar Ajanaku da ke gaban Cocin Salvation Army a kan titin Rukuba, inda suka yi awon gaba da shi da misalin ƙarfe 12:45 na dare a ranar Litinin.




Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *