Jin wa’azi ya sa na yafe wa duk waɗanda na kai kotu saboda ɓata sunana – Akpabio
[ad_1]
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya umarci lauyoyinsa da su janye dukkan ƙararrakin da ya kai wasu mutane kotu bisa zargin su da ɓata suna, bayan jin falalar yafiya daga limamin cocinsa.
Ya ce ya dauki matakin ne bayan jin wa’azin a lokacin taron addu’ar sabuwar shekara.
Yayin da yake jawabi a cocin Sacred Heart Parish da ke Uyo babban birnin jihar Akwa Ibom a ranar Alhamis, Akpabio ya ce ya kai ƙarar ɓata suna kusan tara a kotu kan mutanen da ya zarga da ɓata masa suna.
Ya ce: “Ina da kusan shari’o’i tara a kotu kan wasu mutane da suka ɓata min suna, suka yi min ƙarya, suka yi maganganun da suka lalata sunana. Amma na saurari limamin, sai na fahimci yana magana da ni, don haka na umarci lauyana da ya janye dukkan ƙarar da nake yi a kansu.”
A shekarar 2025, Akpabio ya shigar da ƙarar ɓata suna da dama, ciki har da wadda ta shafi abokiyar aikinsa, Sanata Natasha Akpoti‑Uduaghan.
A ƙarshen shekarar 2025, Akpabio ya shigar da ƙarar ɓata suna ta Naira biliyan 200 a kanta kan zargin cin zarafi, wanda ya musanta, ya kuma bukace ta tabbatar da zargin a kotu.
Tun farkon shekarar, matar Akpabio ma ta shigar da ƙarar ɓata suna a kan Natasha kan zarge-zargen da ta ce sun lalata mutuncin iyalinta.
Dangantaka tsakanin ’yan majalisar biyu ta lalace bayan Natasha ta zargi Akpabio da hannu wajen dakatar da ita daga Majalisar Dattawa a watan Maris 2025, bayan ta yi zargin aikata ba daidai ba a bainar jama’a.
Sanatar ta taɓa kalubalantar matakan da aka ɗauka a kanta a kotu, ciki har da ƙarar ɓata suna ta Naira biliyan 100 da ta shigar a kan Akpabio da wasu, kan maganganun da ta ce sun taba mutuncinta.
Da sanarwar da Akpabio ya yi a ranar Alhamis, yanzu kenan ya kammala janye dukkan shari’o’in da suka shafi ɓata suna, wanda hakan ya nuna kawo ƙarshen rikice-rikicen shari’a da aka yi ta wallafawa a bainar jama’a yayin da sabuwar shekara ta fara.
Masu alaƙa
[ad_2]
Source link