AFCON 2025: Mai masaukin baƙi ta lallasa Comoros

[ad_1]



Ƙasar Maroko wadda ita ce mai masaukin baƙi a Gasar Nahiyar Afirka (AFCON) ta 2025, ta fara da ƙafar dama bayan lallasa Comoros da ci biyu da nema.

An take wasan da misalin ƙarfe 8 na daren ranar Lahadi a filin wasa na Mouley Abdellah da ke Birnin Rabat.

Brahim Diaz ne ya fara saka Maroko a gaba, bayan zura mata ƙwallo a minti na 55, bayan dawowa daga hutun rabin lokaci.

A minti na 74 kuma ɗan wasan gaban Maroko, El Kaabi, ya jefa ƙwallo mai ban mamaki.

Tun farkon fara wasan Maroko ce ta mamaye filin, inda ta dinga kai hare-hare ragar Comoros.

Yanzu haka dai Maroko ce ke jan ragamar rukunin A, da maki 3 yayin da Mali da Zambiya za su ɓarje gumi a ranar Litinin.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *