‘Yansanda Sun Gano Nakiya A Wata Gona A Jihar Borno

[ad_1]

Jami’an rundunar ‘yansandan jihar Borno sun gano wata nakiya da bata tashi ba a wata gona da ke karamar hukumar Dikwa a jihar Borno.

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, ASP Nahum Daso, ya fitar a ranar Litinin, ya ce, rundunar ta samu rahoton ne daga wani Babagana Kachalla, wanda ya ce, ya ga wani abu da yake zargin nakiya ce a gonarsa.

ASP Daso ya ce, bayan samun wannan labari, kwamishinan ‘yansanda na jihar Borno, Naziru Abdulmajid, ya tura kwamandan bincike da warware nakiyoyi da ke sansani na 13, Maiduguri, tare da tawagarsa, zuwa wurin da aka gano nakiyar.

Nakiya

Daso ya kuma tabbatar da cewa, an warware nakiyar cikin nasara ba tare da wata matsala ba.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *