APC ta lashe zaɓen cike gurbi na Ghari/Tsanyawa a Kano




Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta yi nasara a zaɓen cike gurbi na Ghari/Tsanyawa da aka gudanar ranar Asabar a Jihar Kano.

Da yake sanar da sakamakon da misalin karfe 6:10 na safiyar Lahadin nan, babban jami’in da ya tattara sakamakon zaɓen, Farfesa Muhammad Waziri na Jami’ar Bayero, ya bayyana Garba Ya’u Gwarmai na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya yi nasara da ƙuri’u 31,472.

Garba Gwarmai ya kayar da ɗan takarar jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), Yusuf Ali Maigado wanda ya samu ƙuri’u 27,931.




Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *