Babu ƙawancen da NNPP ta ƙulla da wata jam’iyyar — Kwankwaso
[ad_1]
Jagoran jam’iyyar NNPP a Nijeriya, Sanata Rabi’u Kwankwanso, ya ce suna jin daɗin jam’iyyarsu, kuma a halin da ake ciki babu wani ƙawance da suka ƙulla da wata jam’iyyar.
Yayin da yake jawabi a wajen taron majalisar ƙoli na jam’iyyar da aka gudanar a Abuja, Sanata Kwankwaso ya ce ba gaggawa suke yi ba.
Tsohon gwamnan na Kano ya ce kawo yanzu babu wata jam’iyya da suke tattaunawa da ita domin ƙulla ƙawance, sai dai ya ce hakan ba yana nufin ba za su tattauna da wata ba.
“’Yan jam’iyyarmu ba gaggawa suke yi ba, komai muna yinsa a hankali,” in ji shi.
“Muna da jam’iyyarmu (NNPP), kuma ba hanzari muke yi ba. Idan ana so a yi magana da mu babu matsala duk da ba mu manta da abin da aka yi mana a baya ba.
“Mu ’yan siyasa ne kuma a shirye muke mu tattauna da duk wanda ke son tattaunawa da mu.
“Har yanzu jam’iyyarmu na da rawar da za ta iya takawa a mulkin ƙasa,” in ji shi.
An dai jima ana raɗe-raɗin Kwankwaso zai koma jam’iyyar APC, tun bayan zaɓen 2023, inda har aka riƙa hasashen ba shi minista, lokacin da Shugaba Bola Tinubu ya ce zai yi aiki da ’yan hamayya a gwamnatinsa.
Mai dangantaka
[ad_2]
Source link