Ministan Harkokin Waje Tuggar Ya Yi Murabus, Karanta Dalili
[ad_1]
Ministan Harkokin Waje, Yusuf Maitama Tuggar, ya yi murabus daga majalisar ministocin Shugaba Bola Tinubu. Ya ɗauki matakin ne domin neman takarar gwamnan Jihar Bauchi a zaɓen 2027.
Ma’aikatar harkokin wajen ta tabbatar da murabus ɗin ranar Litinin ta bakin mai magana da yawunta, Kimiebi Ebienfa. An ruwaito cewa Tuggar ya miƙa takardar murabus ɗinsa ga shugaban ƙasa da rana.
- Da Sahalewar Nijeriya Bayan Samun Bayanan Sirri Amurka Ta Kai Hari — Tuggar
- Fahimtar Manufofin Nijeriya A Kasashen Waje A Karkashin Tuggar
Rahotanni sun nuna cewa zai nemi tikitin takara ne a ƙarƙashin jam’iyyar APC. Matakin ya biyo bayan umarnin shugaban ƙasa da aka fitar a watan Maris.
Umarnin, ta hannun Sakataren Gwamnatin Tarayya George Akume, ya buƙaci masu riƙe da muƙaman gwamnati su yi murabus. An kayyade ranar ƙarshe zuwa 31 ga Maris, 2026.
Dokar ta shafi ministoci da masu ba da shawara da shugabannin hukumomi. An ce matakin ya dace da sashe na 88(1) na Dokar Zaɓe domin kauce wa rikicin anfani.
[ad_2]
Source link