Peng Liyuan Ta Yi Kiran Daukan Matakin Kasashen Duniya Kan Yaki Da Cutar Tarin Fuka
[ad_1]
Uwargidan shugaban kasar Sin Xi Jinping, Peng Liyuan, kuma jakadiyar hukumar lafiya ta duniya (WHO) game da yaki da cutar tarin fuka da ta HIV/AIDS mai karya garkuwar jiki, ta yi kira ga kasashen duniya da su ba da goyon baya, da kuma shiga a dama da su wajen yaki da cutar tarin fuka a duniya.
A cikin wata sanarwar da aka fitar a rubuce a wani taron da aka yi ta kafar bidiyo domin tunawa da ranar yaki da cutar tarin fuka ta duniya ta WHO a shekarar 2026, Peng ta ce yana da matukar muhimmanci da WHO ta dauki nauyin gudanar da taron ta kafar bidiyo don tattaunawa bisa taken “kasashe ke jagoranta, al’umma ke karfafawa,” domin zai taimaka wajen hada karfi da karfe tsakanin kasashen duniya kan yaki da cutar tarin fuka wadda ta kasance kalubale ga kiwon lafiyar jama’a.
Peng ta kuma ce, bisa jajircewa wajen cimma kudurin kare lafiyar jama’a da cikar burin kawo karshen annobar tarin fuka, hukumar ta WHO ta yi gagarumin aiki mai inganci, tare da shawo kan karuwar bullar cutar tarin fuka da aka samu a baya-bayan nan a duniya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
[ad_2]
Source link