Za mu ceto ’Yan Matan GGCSS Maga cikin ƙoshin lafiya — Gwamnan Kebbi
[ad_1]
Gwamna Ahmed Idris na Jihar Kebbi ya ba da tabbacin cewa jami’an tsaro za su ƙwato ’yan matan da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a Kwalejin ’Yan Mata ta GGCSS Maga da ke Ƙaramar Hukumar Danko Wasu ta jihar cikin ƙoshin lafiya.
Gwamnan ya bayar da tabbacin ne a yayin ganawarsa da iyayen ɗaliban kaɗan bayan harin ’yan bindigar a ranar Litinin.
Aminiya ta ruwaito cewar da asubahin ranar ’yan bindiga suka kusta cikin harabar makarantar kwana ta ’yan mata ta GGCSS Maga, suka kwashe ɗalibai 25 daga ɗakin kwanansu zuwa cikin jeji.
Maharan da suka riƙa harbi a iska kafin su shiga harabar makarantar sun bindige Matakin Shugaban Makarantar, Malam Hassan Yakubu Makuku, wanda ya yi ƙoƙarin hana su tafiya da yaran.
A yayin ziyarar jaje da Gwamna Idris ya kai makarantar, bayan yanke ziyarar aiki da ya kai Abuja, ya ba wa iyayen ɗalibai tabbacin cewa gwamnatinsa da hukumomin tsaro za su yi dukkan abin da zai yiwu wajen ceto yaran.
Kana ya jaddada cewa za su ci ga da ƙoƙari wajen ganin bayan ayyukan ta’addanci a jihar.
Mai dangantaka
[ad_2]
Source link