‘Yan Jarida Su Ne Garkuwar ‘Yan Nijeriya Akan Masu Mulkin Kama-karya — Shettima

[ad_1]


Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ya bayyana ‘yan jaridar Nijeriya a matsayin babbar kariya ga kasar daga mulkin kama-karya, yana mai tabbatar da cewa ‘yancin manema labarai yana nan gaba-gaba a gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

Mataimakin Shugaban Kasa Shettima, ya kara da cewa, ‘yan jarida sun taka rawar gani wajen daidaita rahotanni a lokutan da ake cike da ruɗani da ƙalubale.

Da yake jawabi a ranar Talata a taron shekara-shekara na 2025 da Babban Taron Shekara-shekara na Cibiyar ‘Yan Jarida ta Duniya (IPI) a Najeriya a Abuja, Shettima ya tabbatar da jajircewar gwamnatin tarayya na bai wa masu aikin yada labarai kariya daga masu cin zarafi ko barazana.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *